Harsuna Harsuna
Bayanai masu shiryarwa
SIFFAR AIKIN UMARA
Taƙaitaccen littafin «Siffar Umarah» Na Shehin malami Abdul’Aziz bn Baz - Allah...
TABBATACCAN BAYYANI AKAN YAWANCIN MAS'ALOLIN HAJJI DA UMRA...
كتاب يشتمل على إيضاح وتحقيق لكثيرٍ من مسائل الحج والعمرة والزيارة في ضوء كتاب ال...
TUSHE GUDA UKU DA DALILANSU
TUSHE GUDA UKU DA DALILANSU
Bayanin kafirci da ɓatan duk wanda ya raya...
Bayanin kafirci da ɓatan duk wanda ya raya cewa ya halatta ga wani ya kauce daga...
Ayoyin Al-Kur’anin da aka zaɓa
Lalle ne wannan Alƙur'ãni yanã shiryarwa ga (hãlayen) waɗanda suke mafi daidaita[1] kuma yanã bãyar da bushãra ga mũminai waɗanda suke aikata ayyuka na ƙwarai (cẽwa) "Lalle ne sunã da wata ijãra. mai girma."
Yã kũ mutãne![1] Lalle ne Mũ, Mun halitta ku daga namiji da mace, kuma Muka sanya ku dangõgi da kabĩlõli, dõmin ku san jũna. Lalle mafĩfĩcinku daraja a wurin Allah, (shĩ ne) wanda yake mafĩfĩcinku a taƙawa. Lalle nẽ Allah Masani ne, Mai ƙididdigẽwa.
Hadisan Annabi (SAW) da aka zaɓa
Daga Nu'uman ɗan Bashir - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Kwatankwacin muminai a soyayyarsu da jinkansu da tausayinsu tamkar jiki ne, idan wata gaɓa daga gare shi ta yi ciwo sai ragowar jikin ya ɗauka da rashin bacci da zazzaɓi". [Ingantacce ne] - [Bukhari da Muslim suka ruwaito shi] - [صحيح مسلم - 2586]
Daga Anas ɗan Malik - Allah Ya yarda da shi - daga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Ɗayanku ba zai yi imani ba, har sai ya sowa ɗan uwansa abinda yake sowa kansa". [Ingantacce ne] - [Bukhari da Muslim suka ruwaito shi] - [صحيح البخاري - 13]
Daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Mumini ƙaƙƙarfa ya fi alkairi da soyuwa a wajen Allah sama da mumini rarrauna, akwai alkairi a kowanne, ka yi kwaɗayin yin abinda zai amfane ka, kuma ka nemi taimakon Allah, kada ka gaza, idan wani abu ya sameka kada ka ce: Dana aikata da kaza da kaza ya kasance, sai dai ka ce : Kaddarar Allah abinda Ya so zai aikata, domin cewa (da a ce) tana buɗe aikin Shaidan". [Ingantacce ne] - [Muslim ne ya rawaito shi] - [صحيح مسلم - 2664].
Daga Anas ɗan Malik - Allah Ya yarda da shi - ya ce: "Na ji Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - yana cewa: "Allah - alherinSa ya yawaita kuma Ya ɗaukaka - Ya ce: Yakai ɗan Adam lallai cewa kai muddin ka roƙeNi, ka yi kwaɗayi gareNi zan gafarta maka abinda ya kasance gareka babu ruwaNa". [Hasan ne] - [al-Tirmithi ya ruwaito shi] - [سنن الترمذي - 3540]
Daga Anas - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Mafi yawan addu'ar Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ta kasance: "Ya Allah Ubangijinmu Ka bamu kyakkyawa a duniya, a lahira ma (Ka bamu) kyakkyawa, kuma ka karemu azabar wuta". [Ingantacce ne] - [Bukhari da Muslim suka Rawaito shi] - [ صحيح البخاري - 6389].




