Harsuna Harsuna
Bayanai masu shiryarwa
TUSHE GUDA UKU DA DALILANSU
TUSHE GUDA UKU DA DALILANSU
Kare Tauhidi
Kare Tauhidi
Hukuncin Sihiri da Bokanci da abinda yake da...
Hukuncin Sihiri da Bokanci da abinda yake da alaƙa da su
Ayoyin Al-Kur’anin da aka zaɓa
Hadisan Annabi (SAW) da aka zaɓa
Daga Nu'uman ɗan Bashir - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Kwatankwacin muminai a soyayyarsu da jinkansu da tausayinsu tamkar jiki ne, idan wata gaɓa daga gare shi ta yi ciwo sai ragowar jikin ya ɗauka da rashin bacci da zazzaɓi". [Ingantacce ne] - [Bukhari da Muslim suka ruwaito shi] - [صحيح مسلم - 2586]
Daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Wanda ya yi alwala sai ya kyautata alwala sannan ya zo Juma'a sai ya saurari huduba kuma ya yi shiru yayi saurare za'a gafarta masa abinda ke tsakaninsa da tsakanin Juma'a da ƙarin kwanaki uku, wanda ya taba tsakankwani to haƙiƙa ya yi yashasshiyar magana". [Ingantacce ne] - [Muslim ne ya rawaito shi] - [صحيح مسلم - 857].
Daga Anas - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Mafi yawan addu'ar Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ta kasance: "Ya Allah Ubangijinmu Ka bamu kyakkyawa a duniya, a lahira ma (Ka bamu) kyakkyawa, kuma ka karemu azabar wuta". [Ingantacce ne] - [Bukhari da Muslim suka Rawaito shi] - [ صحيح البخاري - 6389].
Daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Mumini ƙaƙƙarfa ya fi alkairi da soyuwa a wajen Allah sama da mumini rarrauna, akwai alkairi a kowanne, ka yi kwaɗayin yin abinda zai amfane ka, kuma ka nemi taimakon Allah, kada ka gaza, idan wani abu ya sameka kada ka ce: Dana aikata da kaza da kaza ya kasance, sai dai ka ce : Kaddarar Allah abinda Ya so zai aikata, domin cewa (da a ce) tana buɗe aikin Shaidan". [Ingantacce ne] - [Muslim ne ya rawaito shi] - [صحيح مسلم - 2664].
Daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - cewa Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Salloli biyar, da Juma'a zuwa Juma'a, da Ramadan zuwa Ramadan, masu kankare a binda ke tsakaninsu ne idan ya nisanci manyan zunubai". [Ingantacce ne] - [Muslim ne ya rawaito shi] - [صحيح مسلم - 233]




