Harsuna Harsuna
Bayanai masu shiryarwa
SAƘO A KAN JINAYEN ƊABI'A GA MATA
SAƘO A KAN JINAYEN ƊABI'A GA MATA
TUSHE GUDA UKU DA DALILANSU
TUSHE GUDA UKU DA DALILANSU
Manzon Musulunci Annabi Muhammad - tsira da amincin...
Littafin "MANZON MUSULUNCI. (Annabi) Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbat...
Kare Tauhidi
Kare Tauhidi
WA YA HALICCI HALITTU? WA YA HALICCE NI...
Littafin "Wa ya halicci halittu? Kuma wa ya halicceni? Saboda me ?" (Littafin) y...
Ayoyin Al-Kur’anin da aka zaɓa
Yã kũ mutãne![1] Lalle ne Mũ, Mun halitta ku daga namiji da mace, kuma Muka sanya ku dangõgi da kabĩlõli, dõmin ku san jũna. Lalle mafĩfĩcinku daraja a wurin Allah, (shĩ ne) wanda yake mafĩfĩcinku a taƙawa. Lalle nẽ Allah Masani ne, Mai ƙididdigẽwa.
Lalle ne wannan Alƙur'ãni yanã shiryarwa ga (hãlayen) waɗanda suke mafi daidaita[1] kuma yanã bãyar da bushãra ga mũminai waɗanda suke aikata ayyuka na ƙwarai (cẽwa) "Lalle ne sunã da wata ijãra. mai girma."
Hadisan Annabi (SAW) da aka zaɓa
Daga Anas - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Mafi yawan addu'ar Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ta kasance: "Ya Allah Ubangijinmu Ka bamu kyakkyawa a duniya, a lahira ma (Ka bamu) kyakkyawa, kuma ka karemu azabar wuta". [Ingantacce ne] - [Bukhari da Muslim suka Rawaito shi] - [ صحيح البخاري - 6389].
Daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Mumini ƙaƙƙarfa ya fi alkairi da soyuwa a wajen Allah sama da mumini rarrauna, akwai alkairi a kowanne, ka yi kwaɗayin yin abinda zai amfane ka, kuma ka nemi taimakon Allah, kada ka gaza, idan wani abu ya sameka kada ka ce: Dana aikata da kaza da kaza ya kasance, sai dai ka ce : Kaddarar Allah abinda Ya so zai aikata, domin cewa (da a ce) tana buɗe aikin Shaidan". [Ingantacce ne] - [Muslim ne ya rawaito shi] - [صحيح مسلم - 2664].
Daga Anas ɗan Malik - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Ku yi sahur, domin lallai akwai albarka a cikin sahur". [Ingantacce ne] - [Bukhari da Muslim suka ruwaito shi] - [صحيح البخاري - 1923]
Daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Allah Ya ce: Dukkan aikin ɗan Adam nasa ne, sai azumi, lallai shi Nawa ne kuma Nine Zan Yi sakayya da shi ". [Ingantacce ne] - [Bukhari da Muslim suka ruwaito shi] - [صحيح البخاري - 1904]
Daga Anas ɗan Malik - Allah Ya yarda da shi - daga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Ɗayanku ba zai yi imani ba, har sai ya sowa ɗan uwansa abinda yake sowa kansa". [Ingantacce ne] - [Bukhari da Muslim suka ruwaito shi] - [صحيح البخاري - 13]




