Harsuna Harsuna
Bayanai masu shiryarwa
TABBATACCAN BAYYANI AKAN YAWANCIN MAS'ALOLIN HAJJI DA UMRA...
كتاب يشتمل على إيضاح وتحقيق لكثيرٍ من مسائل الحج والعمرة والزيارة في ضوء كتاب ال...
MUHIMMAN DARUSSA GA DUKKANIN AL'UMMA
Littafin Muhimman darussa ga ɗaukacin al'umma na Sheikh Abdul’Aziz Ibnu Bāz - Al...
Manzon Musulunci Annabi Muhammad - tsira da amincin...
Littafin "MANZON MUSULUNCI. (Annabi) Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbat...
TUSHE GUDA UKU DA DALILANSU
TUSHE GUDA UKU DA DALILANSU
SAƘO A KAN JINAYEN ƊABI'A GA MATA
SAƘO A KAN JINAYEN ƊABI'A GA MATA
Ayoyin Al-Kur’anin da aka zaɓa
Lalle ne wannan Alƙur'ãni yanã shiryarwa ga (hãlayen) waɗanda suke mafi daidaita[1] kuma yanã bãyar da bushãra ga mũminai waɗanda suke aikata ayyuka na ƙwarai (cẽwa) "Lalle ne sunã da wata ijãra. mai girma."
Yã kũ mutãne![1] Lalle ne Mũ, Mun halitta ku daga namiji da mace, kuma Muka sanya ku dangõgi da kabĩlõli, dõmin ku san jũna. Lalle mafĩfĩcinku daraja a wurin Allah, (shĩ ne) wanda yake mafĩfĩcinku a taƙawa. Lalle nẽ Allah Masani ne, Mai ƙididdigẽwa.
Hadisan Annabi (SAW) da aka zaɓa
Daga Ɗan Abbas - Allah Ya yarda da su - ya ce: "Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya kasance mafi kyauta cikin mutane, kuma ya kasance mafi kyutar da yake yi a Ramadan ne". [Ingantacce ne] - [Bukhari da Muslim suka ruwaito shi] - [صحيح البخاري - 6]
Daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Wanda ya yi alwala sai ya kyautata alwala sannan ya zo Juma'a sai ya saurari huduba kuma ya yi shiru yayi saurare za'a gafarta masa abinda ke tsakaninsa da tsakanin Juma'a da ƙarin kwanaki uku, wanda ya taba tsakankwani to haƙiƙa ya yi yashasshiyar magana". [Ingantacce ne] - [Muslim ne ya rawaito shi] - [صحيح مسلم - 857].
Daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - cewa Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Salloli biyar, da Juma'a zuwa Juma'a, da Ramadan zuwa Ramadan, masu kankare a binda ke tsakaninsu ne idan ya nisanci manyan zunubai". [Ingantacce ne] - [Muslim ne ya rawaito shi] - [صحيح مسلم - 233]
Daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Allah Ya ce: Dukkan aikin ɗan Adam nasa ne, sai azumi, lallai shi Nawa ne kuma Nine Zan Yi sakayya da shi ". [Ingantacce ne] - [Bukhari da Muslim suka ruwaito shi] - [صحيح البخاري - 1904]
Daga Abu Umamah – Allah Ya yarda da shi – ya ce: -Naji Manzon Allah yana cewa: "Ku karanta Alƙur’ani domin zaizo ranar alƙiyama yana mai ceto ga ma’abotansa". [Ingantacce ne] - [Muslim ne ya ruwaito shi]




