Harsuna Harsuna
Bayanai masu shiryarwa
WA YA HALICCI HALITTU? WA YA HALICCE NI...
Littafin "Wa ya halicci halittu? Kuma wa ya halicceni? Saboda me ?" (Littafin) y...
MUHIMMAN DARUSSA GA DUKKANIN AL'UMMA
MUHIMMAN DARUSSA GA DUKKANIN AL'UMMA
Kare Tauhidi
Kare Tauhidi
Dalilin Hukuncin mai neman agaji ga wanin Allah
Dalilin Hukuncin mai neman agaji ga wanin Allah
Ayoyin Al-Kur’anin da aka zaɓa
Lalle ne wannan Alƙur'ãni yanã shiryarwa ga (hãlayen) waɗanda suke mafi daidaita[1] kuma yanã bãyar da bushãra ga mũminai waɗanda suke aikata ayyuka na ƙwarai (cẽwa) "Lalle ne sunã da wata ijãra. mai girma."
Yã kũ mutãne![1] Lalle ne Mũ, Mun halitta ku daga namiji da mace, kuma Muka sanya ku dangõgi da kabĩlõli, dõmin ku san jũna. Lalle mafĩfĩcinku daraja a wurin Allah, (shĩ ne) wanda yake mafĩfĩcinku a taƙawa. Lalle nẽ Allah Masani ne, Mai ƙididdigẽwa.
Hadisan Annabi (SAW) da aka zaɓa
Daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - cewa Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya ce: "Salloli biyar, da Juma'a zuwa Juma'a, da Ramadan zuwa Ramadan, masu kankare a binda ke tsakaninsu ne idan ya nisanci manyan zunubai". [Ingantacce ne] - [Muslim ne ya rawaito shi] - [صحيح مسلم - 233]
Daga Anas ɗan Malik - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Ku yi sahur, domin lallai akwai albarka a cikin sahur". [Ingantacce ne] - [Bukhari da Muslim suka ruwaito shi] - [صحيح البخاري - 1923]
Daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Allah Ya ce: Dukkan aikin ɗan Adam nasa ne, sai azumi, lallai shi Nawa ne kuma Nine Zan Yi sakayya da shi ". [Ingantacce ne] - [Bukhari da Muslim suka ruwaito shi] - [صحيح البخاري - 1904]
Daga Anas - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Mafi yawan addu'ar Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ta kasance: "Ya Allah Ubangijinmu Ka bamu kyakkyawa a duniya, a lahira ma (Ka bamu) kyakkyawa, kuma ka karemu azabar wuta". [Ingantacce ne] - [Bukhari da Muslim suka Rawaito shi] - [ صحيح البخاري - 6389].
Daga Ɗan Abbas - Allah Ya yarda da su - ya ce: "Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya kasance mafi kyauta cikin mutane, kuma ya kasance mafi kyutar da yake yi a Ramadan ne". [Ingantacce ne] - [Bukhari da Muslim suka ruwaito shi] - [صحيح البخاري - 6]




