إِقََامَةُ البَرَاهِينِ عَلَى
حُكْمِ مَنِ اسْتَغَاثَ بِغَيرِ اللهِ
Dalilin Hukuncin mai neman agaji ga wanin Allah
لِسَمَاحَةِ الشَّيْخِ العَلَّامَةِ
عَبْدِ العَزِيزِ بْنِ عَبْدِ اللهِ بْنِ بَازٍ
رَحِمَهُ اللهُ
Wallafar: Babban Malami
AbdulAzeez Bin Abdullahi Bin Baaz
Allah Yayi masa rahama
بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَنِ الرَّحِيمِ
SAƘO NA BIYU
Akan hukuncin neman agaji da Annabi
-tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -.
Godiya ta tabbata ga Allah, tsira da amincin Allah su tabbata ga Manzon Allah, da alayen sa da sahabban sa da waɗanda suka shiryu da shiriyar sa.
Bayan haka: haƙiƙa jaridar zamantakewa ta ƙasar Kuwait a fitowa ta 15, ranar 19/4/1390 bayan hijira, ta buga wani bayani a ƙarƙashin matashiyar: (Tunawa da mauludin Annanbi mai daraja), to waɗannan baitukan sun kasance suna ƙunshe da neman agajin Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - da neman taimakon sa; domin ya kawowa wannan al’umma ɗauki, ya taimaketa ya tsamar da ita daga inda ta afka na rarrabuwa da saɓani. Wacce ta rattaba hannu ita ce: (Amina), ga nassin baitocin da aka yi maganar a cikin su:
Ya Manzon Allah, ka ceci wani malami... yana rura wutar yaƙi kuma yana ƙonewa daga wutarta
Ya Manzon Allah, ka ceci wata al'umma... cikin duhun shakka, da sirrin ta ya tsawaita.
Ya Manzon Allah, ka ceci wata al'umma... a cikin ruɗanin baƙin da hangen nesanta ya ɓace
Har zuwa inda tace:
Ka gaggauta taimako, kamar yadda Ka gaggauta shi... a ranar Badar lokacin da ka kira Allah.
Sabõda haka, ƙasƙanci ya koma taimako mai ban mamaki... Lalle ne Allah Yana da rundunõni waɗanda ba ka ganinsu.
(Haka mai wannan rubutun take fuskantar da kiran ta da neman agajin ta zuwa ga Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -, tana neman ya kawowa wannan al’umma ɗauki ta hanyar gaggauto da nasara -.Ta manta - ko ta jahilci - cewa nasara tana hannun Allah ne Shi kaɗai, ba tana hannun Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ba ne, ko wanin sa a cikin halittu, kamar yanda Allah - tsarki ya tabbata a gare Shi - Ya ce a littafin Sa mabayyani:
﴿...وَمَا النَّصْرُ إِلَّا مِنْ عِنْدِ اللَّهِ الْعَزِيزِ الْحَكِيمِ﴾
{Taimako bai kasance ba fãce daga wurin Allah, Mabuwãyi, Mai hikima} [Aali- Imran: 126], Kuma Allah - Maɗaukaki - Ya ce:
﴿إِنْ يَنْصُرْكُمُ اللَّهُ فَلَا غَالِبَ لَكُمْ وَإِنْ يَخْذُلْكُمْ فَمَنْ ذَا الَّذِي يَنْصُرُكُمْ مِنْ بَعْدِهِ...﴾
{Idan Allah Ya taimake ku, to, bãbu marinjayi a gare ku. Kuma idan Ya yarɓe ku, to, wãnẽ ne wanda yake taimakon ku a bāyanSa} [Aali- Imran: 160].
Wannan aiki na roƙo da neman agaji, shi ne: juyar da nau’i daga cikin nau’ikan ibada ga wanin Allah - Maɗaukakin Sarki -; Haƙiƙa an sani da Nassi da kuma Ijima’i: Lalle hakan bai halatta ba, kuma Allah - tsarki ya tabbata a gare Shi - Ya halicci halitta ne domin su bauta maSa, kuma Ya aiko da Manzanni, Ya kuma saukar da littattafai domin bayanin wannan ibadar da kuma kira zuwa gare ta, kamar yadda (Allah) - tsarki ya tabbata a gare shi - Ya ce:
﴿وَمَا خَلَقْتُ الْجِنَّ وَالْإِنْسَ إِلَّا لِيَعْبُدُونِ56﴾
{Kuma Ban halitta aljannu da mutãne ba sai dõmin su bauta Mini} [al-Zariyat: 56], Kuma Allah - Maɗaukakin Sarki - Ya ce:
﴿وَلَقَدْ بَعَثْنَا فِي كُلِّ أُمَّةٍ رَسُولًا أَنِ اُعْبُدُوا اللَّهَ وَاجْتَنِبُوا الطَّاغُوتَ...﴾
{Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun aika a cikin kõwace al'umma da wani Manzo (ya ce): "Ku bauta wa Allah, kuma ku nĩsanci ɗãgũtu} [al-Nahl: 36], Kuma Allah - Maɗaukakin Sarki - Ya ce:
﴿وَمَا أَرْسَلْنَا مِنْ قَبْلِكَ مِنْ رَسُولٍ إِلَّا نُوحِي إِلَيْهِ أَنَّهُ لَا إِلَهَ إِلَّا أَنَا فَاعْبُدُونِ25﴾
{Kuma ba Mu aiki wani Manzo ba a gabãninka fãce Munã yin wahayi zuwa gare shi, cẽwa "Lalle ne Shi, bãbu abin bautãwa fãce Nĩ, sai ku bauta Mini} [al-Anbiya'a: 25], Kuma Allah - Maɗaukaki - Ya ce:
﴿الر كِتَابٌ أُحْكِمَتْ آيَاتُهُ ثُمَّ فُصِّلَتْ مِنْ لَدُنْ حَكِيمٍ خَبِيرٍ1 أَلَّا تَعْبُدُوا إِلَّا اللَّهَ إِنَّنِي لَكُمْ مِنْهُ نَذِيرٌ وَبَشِيرٌ2﴾
{A. L̃.R. Littãfi ne an kyautata ãyõyinsa, sa'an nan an bayyanã su daki-daki, daga wurin Mai hikima, Mai ƙididdigewa}
{Kada ku bautã wa kõwa fãce Allah. Lalle ne ni a gare ku mai gargaɗi ne kuma mai bushãrã daga gare Shi} [Hud: 1, 2].
Sai (Allah) - Maɗaukakin Sarki - Ya yi bayani a waɗannan ayoyin bayyanannu cewa, bai halicci mutum da aljan ba sai domin su bauta maSa Shi kaɗai, ba Shi da abokin tarayya, kuma Ya bayyana cewa Ya aiko manzanni ne - tsira da aminci ya tabbata a gare su - domin umarni da wannan ibadar, da kuma hani daga kishiyar ta, kuma Allah - Mai girma da ɗaukaka - Ya bada labarin cewa Ya kyautata ayoyin littafinSa, kuma Ya rabe su daki-daki domin kada a bautawa wani wanda ba Shi ba - tsarki ya tabbata a gare Shi -.
Sananne ne ibada tana nufin: Kaɗaita Allah da kuma Yi maSa ɗa'a, ta yin ruƙo da umarninSa da kuma barin abubuwan da Ya hana, kuma haƙiƙa Allah Ya yi umarni Ya kuma bada labari da hakan a ayoyi masu yawa, daga cikin su: FaɗinSa - tsarki ya tabbata a gare Shi -:
﴿وَمَا أُمِرُوا إِلَّا لِيَعْبُدُوا اللَّهَ مُخْلِصِينَ لَهُ الدِّينَ حُنَفَاءَ...﴾
{Kuma ba a umarce su da kome ba fãce bauta wa Allah suna mãsu tsarkake addinin gare Shi, mãsu karkata zuwa ga addinin gaskiya} [al-Bayyinah: 5], Da faɗinSa - Mai girma da ɗaukaka -:
﴿وَقَضَى رَبُّكَ أَلَّا تَعْبُدُوا إِلَّا إِيَّاهُ...﴾
{Kuma Ubangijinka Ya hukunta kada ku bauta wa kõwa fãce Shi} [al-Isra'a: 23], Da faɗinSa - tsarki ya tabbatar maSa -:
﴿إِنَّآ أَنزَلۡنَآ إِلَيۡكَ ٱلۡكِتَٰبَ بِٱلۡحَقِّ فَٱعۡبُدِ ٱللَّهَ مُخۡلِصٗا لَّهُ ٱلدِّينَ2 أَلَا لِلَّهِ ٱلدِّينُ ٱلۡخَالِصُۚ وَٱلَّذِينَ ٱتَّخَذُواْ مِن دُونِهِۦٓ أَوۡلِيَآءَ مَا نَعۡبُدُهُمۡ إِلَّا لِيُقَرِّبُونَآ إِلَى ٱللَّهِ زُلۡفَىٰٓ إِنَّ ٱللَّهَ يَحۡكُمُ بَيۡنَهُمۡ فِي مَا هُمۡ فِيهِ يَخۡتَلِفُونَۗ إِنَّ ٱللَّهَ لَا يَهۡدِي مَنۡ هُوَ كَٰذِبٞ كَفَّارٞ3﴾
{Mun saukar da littafi a gareka da Gaskiya ka bautawa Allah kana mai tsarkake Addini a gare shi}
{To, addini tsarkakakke na Allah ne, kuma waɗanda suka riƙi waɗansu majibinta, bã Shi ba, (sunã cẽwa) "Ba mu bauta musu ba fãce dõmin su kusantar da mu zuwa ga Allah, kusantar daraja." Lalle Allah nã yin hukunci a tsakãninsu ga abin da suka zama sunã sãɓãwa a cikinsa. Lalle Allah ba Ya shiryar da wanda yake mai ƙarya, mai kãfirci} [al-Zumar: 2-3].
Ayoyi a wannan ma’anar suna da yawa, kuma dukkan su suna nuni akan wajabcin tsarkake ibada domin Allah Shi kaɗai, da barin bautawa wanda ba Shi ba cikin Annabawa da wasun su.
Babu shakka, ita addu’a tana daga muhimman nau’ikan ibada kuma mafi tattarar su, sai ya wajaba a tsarkake ta domin Allah Shi kaɗai, kamar yadda Allah - Mai girma da ɗaukaka - Ya ce:
﴿فَادْعُوا اللَّهَ مُخْلِصِينَ لَهُ الدِّينَ وَلَوْ كَرِهَ الْكَافِرُونَ14﴾
{Sabõda haka ku kirãyi Allah, kunã mãsu tsarkake addini a gare Shi, kuma kõ dã kãfirai sun ƙi} [Ghafir: 14], Kuma (Allah) - Mai girma da ɗaukaka - Ya ce-:
﴿وَأَنَّ الْمَسَاجِدَ لِلَّهِ فَلَا تَدْعُوا مَعَ اللَّهِ أَحَدًا18﴾
{Kuma lalle ne wurãren sujada na Allah ne, saboda haka kada ku kira kõwa tãre da Allah (da su, a cikinsu)} [al-Jinn: 18], Wannan fuskantarwar, ta kaɗaita Allah da addu’a tana game dukkanin halitta daga Annabawa da wasunsu, fadinSa (Allah):
﴿وَلَا تَدْعُ مِنْ دُونِ اللَّهِ مَا لَا يَنْفَعُكَ وَلَا يَضُرُّكَ فَإِن فَعَلۡتَ فَإِنَّكَ إِذٗا مِّنَ ٱلظَّٰلِمِينَ106﴾
{Kuma kada ka kirãyi, baicin Allah, abin da bã ya amfãnin ka kuma bã ya cũtar ka. To, idan ka aikata haka, sa'an nan lalle kai, a lõkacin, kanã daga mãsu zãlunci.} [Yunus: 106], Wannan magana ce ga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -, kuma sanannen abu ne cewa Allah - Maɗaukakin Sarki - Ya tsare shi daga shirka, kawai dai abin nufi da wannan shine tsoratar da waninsa. Sannan Allah - Maɗaukakin Sarki - Ya ce:
﴿وَلَا تَدۡعُ مِن دُونِ ٱللَّهِ مَا لَا يَنفَعُكَ وَلَا يَضُرُّكَ فَإِنْ فَعَلْتَ فَإِنَّكَ إِذًا مِنَ الظَّالِمِينَ106﴾
{"Kuma kada ka kirãyi, baicin Allah, abin da bã ya amfãnin ka kuma bã ya cũtar ka. To, idan ka aikata haka, sa'an nan lalle kai, a lõkacin, kanã daga mãsu zãlunci."} [Yunus: 106], Kuma wannan kira ne ga Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -, kuma abin nufi shi ne: Tsawatar da waninsa; domin sanannen abu ne, Allah - Maɗaukakin Sarki - haƙiƙa ya tsare Manzon sa daga shirka, sannan kuma Allah - Maɗaukakin Sarki - Ya kausasa hanin da tsawatarwar, sai Ya ce:
﴿...فَإِنْ فَعَلْتَ فَإِنَّكَ إِذًا مِنَ الظَّالِمِينَ﴾
{To idan ka aikata, to lalle kai a lokacin kana cikin azzalumai} Shi zalunci idan aka faɗe shi a sake, to ana nufin: Babbar shirka, kamar yadda (Allah) - Maɗaukakin Sarki - Ya ce:
﴿...وَالْكَافِرُونَ هُمُ الظَّالِمُونَ﴾
{Kuma kãfirai sũ ne azzãlumai} [al-Baƙara: 254] Kuma Allah - Maɗaukakin Sarki - Ya ce:
﴿...إِنَّ الشِّرْكَ لَظُلْمٌ عَظِيمٌ﴾
{Lalle shirki wani zãlunci ne mai girma} [Luƙman: 13]. Har idan shugaban ‘yan Adam - tsira da aminci su tabbata a gare shi -, da zai kira wanin Allah zai kasance cikin azzalumai, to ina ga wanda ba shi ba?!.
Sai aka sani da waɗannan ayoyin da wasunsu, lalle kiran wanin Allah - daga matattu da bishiyoyi da gumaka da wasunsu -, shirka ne da Allah - Maɗaukakin Sarki -, kuma yana kore kaɗaita Allah a ibada wacce take ita ce manufar halittar mutum da aljan, da kuma aiko Manzanni da saukar da littattafai, kuma mai cin karo ce ga ma’anar: Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, wacce take kore bautawa wanin Allah, take kuma tabbatar da ita ga Allah Shi kaɗai, kamar yadda Allah - Maɗaukakin Sarki - Ya ce:
﴿ذَٰلِكَ بِأَنَّ ٱللَّهَ هُوَ ٱلۡحَقُّ وَأَنَّ مَا يَدۡعُونَ مِن دُونِهِۦ هُوَ ٱلۡبَٰطِلُ وَأَنَّ ٱللَّهَ هُوَ ٱلۡعَلِيُّ ٱلۡكَبِيرُ62﴾
{Wancan! sabõda lalle ne Allah, shĩ ne Gaskiya, kuma lalle ne, abin da suke kira waninSa shi ne ƙarya. Kuma lalle ne Allah, Shĩ ne Maɗaukaki, Mai girma} [al-Hajj: 62].
Wannan shi ne asalin Addini kuma tushen al'umma, kuma ibadu ba zasu inganta ba sai bayan ingancin wannan asali, kamar yadda
- Maɗaukakin Sarki - Ya ce:
﴿وَلَقَدْ أُوحِيَ إِلَيْكَ وَإِلَى الَّذِينَ مِنْ قَبْلِكَ لَئِنْ أَشْرَكْتَ لَيَحْبَطَنَّ عَمَلُكَ وَلَتَكُونَنَّ مِنَ الْخَاسِرِينَ65﴾
{Kuma an yi wahayi zuwa gare ka da kuma zuwa ga waɗanda suke a gabãninka, "Lalle idan ka yi shirki haƙĩƙa aikinka zai ɓãci, kuma lalle zã ka kasance daga mãsu hasãra} [al-Zumar: 65], (Allah) - Mai tsarki da ɗaukaka - Ya ce:
﴿...وَلَوْ أَشْرَكُوا لَحَبِطَ عَنْهُمْ مَا كَانُوا يَعْمَلُونَ﴾
{Kuma dã sun yi shirki dã haƙĩƙa abin da suka kasance sunã, aikatãwa yã lãlãce} [al-An'am: 88].
Daga cikin abinda ya gabata, yana bayyana cewa Addinin Musulinci da shaidawa (Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah), suna da tushe guda biyu masu girma:
Na farkon su: Kada abautawa kowa sai Allah Shi kaɗai, ba Shi da abokin tarayya; wanda ya kira matattu daga cikin Annabawa da wasunsu, ko ya kira gumaka ko bishiyoyi ko duwatsu ko wasunsu cikin halittu, ko ya nemi agajin su ko ya nemi kusanci zuwa gare su ta hanyar yanka ko bakance, ko ya yi musu sallah ko ya yi musu sujjada; to haƙiƙa ya ɗauke su abubuwan bauta koma bayan Allah, ya kuma sanya su kishiyoyi gare Shi - Mai tsarki da ɗaukaka -, ya kuma warware da kore ma’anar: Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah.
Na biyu: Kada a bautawa Allah saida shari’ar AnnabinSa kuma ManzonSa, - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -, duk wanda ya ƙirƙiro wata bidi’a a addini wacce Allah Bai yi izini da ita ba; to bai tabbatar da ma’anar shaidawa cewa (Annabi) Muhammad Manzon Allah ne ba, kuma aikin sa ba zai anfane shi ba, kuma ba za’a karɓi aikin daga wurin sa ba, Allah - girman Sa ya ɗaukaka - Ya ce:
﴿وَقَدِمْنَا إِلَى مَا عَمِلُوا مِنْ عَمَلٍ فَجَعَلْنَاهُ هَبَاءً مَنْثُورًا23﴾
{Kuma Muka gabãta zuwa ga abin da suka aikata daga aiki, sai Muka sanya shi ƙũra wãtsattsiya} [al-Furƙan: 23], Abin nufi da waɗannan ayyukan da aka ambata a ayar: Ayyukan wanda ya mutu yana shirka da Allah - Mai girma da ɗaukaka -.
Yana shiga ciki kuma: Ayyukan da aka ƙirƙira, waɗanda Allah Bai bada izini ba, domin za su kasance ranar lahira tamkar ƙura watsattsiya, saboda kasantuwar su ba su yi daidai da Shari’a tsarkakkiya ba, kamar yadda Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: «Duk wanda ya farar da wani sabon abu a cikin wannan addinin namu wanda ba ya ciki, to shi abun mayarwa ne». Bukhari da Muslim sun haɗu akan ingancinsa.
A taƙaice dai: Wannan mai rubutun ta nemi ta fuskantar da neman agajin ta ne da roƙon ta ga Ma’aikin - Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -, ta kau da kai daga Allah Ubangijin talikai, wanda a hannunSa taimako da cuta da amfani yake, babu wani abu daga wannan da yake a hannun wani wanda ba shi ba.
Babu shakka lalle wannan zalunci ne mai girma kuma mai muni, haƙiƙa Allah - Mai girma da ɗaukaka - Ya yi umarni da a roƙe Shi, kuma ya yiwa wanda ya roƙe Shi alƙawarin amsawa, Ya kuma yi alƙawarin narkon azaba ga wanda ya yi girman kai daga barin hakan (roƙon Shi) da shiga Jahannama, kamar yadda Allah - Mai girma da ɗaukaka - Ya ce:
﴿وَقَالَ رَبُّكُمُ ادْعُونِي أَسْتَجِبْ لَكُمْ إِنَّ الَّذِينَ يَسْتَكْبِرُونَ عَنْ عِبَادَتِي سَيَدْخُلُونَ جَهَنَّمَ دَاخِرِينَ 60﴾
{Kuma Ubangijinku ya ce: "Ku kira Ni in karɓa muku. Lalle waɗannan da ke kangara daga barin bauta Mini, za su shiga Jahannama sunã ƙasƙantattu} [Gafir: 60], Wato: ƙasƙantattu wulaƙantattu, Sai waɗannan ayoyin masu karamci suka yi nuni akan lalle addu’a ibada ce, kuma duk wanda ya yi girman kai daga gare ta, to makomar sa Jahannama ce, idan wannan shi ne halin wanda ya yi girman kai daga roƙon Allah, to ya halin wanda ya roƙi waninSa, ya bijire maSa (Allah), alhali Shi - tsarki ya tabbata a gare Shi - Makusanci ne, Mamallakin kowanne abu, Mai iko ne akan komai, kamar yadda Allah - tsarki ya tabbata a gare Shi - Ya ce:
﴿وَإِذَا سَأَلَكَ عِبَادِي عَنِّي فَإِنِّي قَرِيبٌ أُجِيبُ دَعْوَةَ الدَّاعِ إِذَا دَعَانِ فَلْيَسْتَجِيبُوا لِي وَلْيُؤْمِنُوا بِي لَعَلَّهُمْ يَرْشُدُونَ 186﴾
{Kuma idan bãyiNa suka tambaye ka daga gare Ni, to, lalle Ni Makusanci ne. Ina karɓa kiran mai kira idan ya kirã Ni. Sabõda haka su nẽmi karɓawaTa, kuma su yi ĩmãni da Ni: tsammãninsu, su shiryu} [al-Baƙara: 186], Kuma Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ba da labari a cikin hadisi sahihi cewa addu'a ita ce ibada, kuma ya ce wa ɗan kawunsa Abdullahi bin Abbas - yardar Allah ta tabbata a gare su: «Ka kiyaye Allah sai Allah Ya kiyaye ka, ka kiyaye Allah sai ka same Shi duk halin da kasamu kanka, kuma idan zakayi roƙo, to, ka roƙi Allah, kuma idan zaka nemi taimako to ka nemi taimakon Allah». Tirmizi da wanin sa ne suka fitar da shi.
Kuma - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: «Duk wanda ya mutu yana kiran wani kini ga Allah, to zai shiga wuta». Bukhari ne ya rawaito shi, A cikin Sahih Bukhari da Muslim, an rawaito daga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - cewa an tambaye shi: Wanne zunubi ne ya fi girma? Ya ce: «Ka sanyawa Allah kini alhali kuwa shi ne ya halliceka?». Al-Niddu: Shine makamanci da mamisalci, don haka duk wanda ya kira wanin Allah, ko ya nemi taimako daga gare shi ko yayi bakance saboda shi, ko yayi masa yanka, ko ya juya wata ibada zuwa gare shi banda abin da ya gabata; to ya ɗauke shi a matsayin abokin tarayya, daidai ne ya kasance Annabi ne, ko waliyi, ko mala'ika, ko aljani, ko gunki, ko wanin haka daga cikin halittu.
A nan kuma takan yi wu mai tambaya ya ce: To menene hukuncin roƙon wanda yake a raye mahalarci akan abinda yake da iko akai, da kuma neman taimakon sa a kan abubuwan da ake gani ko ake taɓawa waɗanda yake da iko akan su; Amsa a nan: Wannan ba shi daga cikin shirka, kawai yana cikin lamurra na al’ada da suke halas ne tsakanin musulmai, kamar yadda Allah - Maɗaukakin Sarki - Ya faɗa a ƙissar Annabi Musa:
﴿...فَاسْتَغَاثَهُ الَّذِي مِنْ شِيعَتِهِ عَلَى الَّذِي مِنْ عَدُوِّهِ...﴾
{Sai wannan da yake daga ƙungiyarsa ya nẽmi ãgajinsa akan wanda yake daga maƙiyansa} [al-Ƙasas: 15], Kuma kamar yadda - Maɗaukakin Sarki - Ya ce a cikin labarin Musa ma:
﴿فَخَرَجَ مِنْهَا خَائِفًا يَتَرَقَّبُ...﴾
{Sai ya fita daga gare ta,* yanã mai jin tsõro yanã sauna} [al-Ƙasas: 21], Kuma kamar yadda mutum yake neman agajin abokan sa a yaƙi, da wanin hakan na lamuran da suke bujurowa mutane, ya zama sashen su yana buƙatar sashe.
Kuma haƙiƙa Allah Ya umarci AnnabinSa - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - da ya baiwa al’ummar sa labarin shi fa ba ya mallakar amfani ko cuta ga kowa, sai (Allah) - Mai tsarki da ɗaukaka - Ya ce:
﴿قُلْ إِنَّمَا أَدْعُو رَبِّي وَلَا أُشْرِكُ بِهِ أَحَدًا21 قُلْ إِنِّي لَا أَمْلِكُ لَكُمْ ضَرًّا وَلَا رَشَدًا22﴾
{Ka ce: "lna kiran Ubangijina ne kawai, kuma bã zan tãra kowa da Shi ba. Ka ce: "Lalle ne, nĩ bã ni mallakar wata cũta gare ku, kuma bã ni mallakar wani alhẽri."}
Ka ce: "Lalle ne, nĩ bã ni mallakar wata cũta gare ku, kuma bã ni mallakar wani alhẽri. [al-Jinn: 21,22], Kuma Allah - Maɗaukakin Sarki - Ya ce:
﴿قُلْ لَا أَمْلِكُ لِنَفْسِي نَفْعًا وَلَا ضَرًّا إِلَّا مَا شَاءَ اللَّهُ وَلَوْ كُنْتُ أَعْلَمُ الْغَيْبَ لَاسْتَكْثَرْتُ مِنَ الْخَيْرِ وَمَا مَسَّنِيَ السُّوءُ إِنْ أَنَا إِلَّا نَذِيرٌ وَبَشِيرٌ لِقَوْمٍ يُؤْمِنُونَ188﴾
{Ka ce: "Bã ni mallaka wa raina wani amfãni, kuma haka ban tunkuɗe wata cũta, fãceabin da Allah Ya so. Kuma dã na kasance inã sanin gaibi, dã lalle ne, nã yawaita daga alhẽri kuma cũta bã zã ta shãfe ni ba, nĩ ban zama ba fĩce mai gargaɗi, kumamai bãyar da bishãra ga mutãne waɗanda suke yin ĩmãni} [al-A'araf: 188].
Kuma ayoyi da suka zo da wannan ma’anar suna da yawa.
Kuma sanannen abu ne, lalle Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -, ba ya kiran kowa sai Ubangijin sa, kamar yadda ya tabbata daga gare shi ya kasance a ranar (yaƙin) Badar yana neman agajin Allah ne, yana neman taimakon Sa akan abokan gabar sa, yana marairaicewa akan hakan, yana cewa: «Ya Ubangiji! Ka zartar min abinda Ka yi min alƙawarin sa». Har ya kai babban abokin sa, Abubakar - Allah Ya yarda da shi - Ya ce: Allah Ya isar maka Ya Ma’aikin Allah, lalle Allah Zai zartar maka alƙawarin da Ya yi maka, kuma Allah - Maɗaukakin Sarki - Ya saukar da faɗinSa a akan hakan:
﴿إِذۡ تَسۡتَغِيثُونَ رَبَّكُمۡ فَٱسۡتَجَابَ لَكُمۡ أَنِّي مُمِدُّكُم بِأَلۡفٖ مِّنَ ٱلۡمَلَٰٓئِكَةِ مُرۡدِفِينَ9﴾
{A lõkacin da kuke nẽman Ubangijinku taimako, sai Ya karɓa muku cẽwa: "Lalle ne Nĩ, Mai taimakon ku ne da dubu daga malã'iku, jẽre} [al-Anfal: 9]. Sai (Allah) - Maɗaukakin Sarki - Ya ambata musu neman agajin su a wannan ayar, Ya kuma labarta cewa Ya amsa musu, Sai ya ƙarfafe su da Mala’iku; domin bada bushara da nasara da kuma kwanciyar hankali, kuma (Allah) - tsarki ya tabbata a gare shi -Ya yi bayanin lalle ita nasarar ba daga Mala’iku take ba, ita nasara daga wurin Allah take, sai (Allah) - Maɗaukakin Sarki - Ya ce:
﴿وَمَا النَّصْرُ إِلَّا مِنْ عِنْدِ اللَّهِ...﴾
{Taimako bai kasance ba fãce daga wurin Allah} [Aali- Imran: 126], Kuma Allah - Maɗaukaki - Ya ce:
﴿وَلَقَدْ نَصَرَكُمُ اللَّهُ بِبَدْرٍ وَأَنْتُمْ أَذِلَّةٌ فَاتَّقُوا اللَّهَ لَعَلَّكُمْ تَشْكُرُونَ123﴾
{Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Allah Yã taimake ku a Badar, alhãli kuwa kunã mafiya rauni, sabõda haka ku bi Allah da taƙawa tsammãninku, kuna gõdẽwa} [Aal- Imran: 123]. Sai (Allah) - tsarki ya tabbata a gare Shi - Ya yi bayani a cikin waɗannan ayoyin, Shi ne Mai basu nasara a ranar (yaƙin) Badar, sai aka sani da wannan cewa, abinda Ya ba su na makamai da ƙarfi, da kuma abinda Ya ƙarfafe su da shi na Mala’iku, duka yana cikin sabubba ne na samun nasara da bushara da natsuwa, ba wai nasara daga Mala’ikun ba ne, kawai ita nasara daga wurin Allah take shi kaɗai. To, ta yaya wannan mai rubutun ta yi ƙarfin hali ko ma wanin ta, ta fuskantar da neman agajin ta da neman nasarar ta daga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -, ta juya baya daga Ubangijin talikai, Mamallakin kowanne abu, Mai iko akan dukkan komai?!
Babu shakka lallai wannan yana cikin mafi munin jahilci, kai yana cikin mafi munin shirka ma, to abinda ya zama wajibi ga ita mai wannan rubutun shi ne ta tuba zuwa ga Allah - tsarki ya tabbata a agare Shi -, tuba na gaskiya, tuba na gaskiya kuwa shi ne wanda ya ƙunshi abubuwa da dama, su ne kamar haka: Na farko: Nadama akan abinda ya afku daga garesu. Na biyu: Cirata daga abinda ya afka ɗin. Na uku: Niyyar ba zai sake komawa ga saɓon ba, domin girmama Allah da tsarkake addini gare Shi, da kuma kamantawa da umarnin Sa, da kiyayewa akan abinda Ya hana, wannan shi ne tuba mai kyau, Akwai kuma wani lamari na huɗu, shi na daban ne, idan saɓon ya kasance a haƙƙin halittu ne, shi ne:
Na hudu: Mayar da haƙƙi ga masu haƙƙin su, ko ya warware shi daga gare shi.
Kuma haƙiƙa Allah Ya umarci bayinSa da (su) tuba, kuma Ya yi musu alkawarin karɓar ta, kamar yadda Allah - Maɗaukakin Sarki - Ya ce:
﴿وَتُوبُوا إِلَى اللَّهِ جَمِيعًا أَيُّهَ الْمُؤْمِنُونَ لَعَلَّكُمْ تُفْلِحُونَ31﴾
{Kuma ku tũba zuwa ga Allah gabã ɗaya, yã ku mũminai! Tsammãninku, ku sãmi babban rabo} [al-Nur: 31], Kuma (Allah - Madaukakin Sarki -) Yace game da kiristoci:
﴿أَفَلَا يَتُوبُونَ إِلَى اللَّهِ وَيَسْتَغْفِرُونَهُ وَاللَّهُ غَفُورٌ رَحِيمٌ74﴾
{Shin fã, bã su tuba zuwa ga Allah, kuma su neme Shi gãfara, alhãli kuwa Allah Mai gãfara ne, Mai jin ƙai?} [al-Ma'ida: 74], Kuma Allah - Maɗaukakin Sarki - Ya ce:
﴿وَالَّذِينَ لَا يَدْعُونَ مَعَ اللَّهِ إِلَهًا آخَرَ وَلَا يَقْتُلُونَ النَّفْسَ الَّتِي حَرَّمَ اللَّهُ إِلَّا بِالْحَقِّ وَلَا يَزْنُونَ وَمَنْ يَفْعَلْ ذَلِكَ يَلْقَ أَثَامًا68 يُضَاعَفْ لَهُ الْعَذَابُ يَوْمَ الْقِيَامَةِ وَيَخْلُدْ فِيهِ مُهَانًا69 إِلَّا مَنْ تَابَ وَآمَنَ وَعَمِلَ عَمَلًا صَالِحًا فَأُولَئِكَ يُبَدِّلُ اللَّهُ سَيِّئَاتِهِمْ حَسَنَاتٍ وَكَانَ اللَّهُ غَفُورًا رَحِيمًا70﴾
{Kuma waɗanda bã su kiran wani ubangiji tãre da Allah, kuma bã su kashe rai wanda Allah Ya haramta fãce da haƙƙi kuma bã su yin zina. Kuma wanda ya aikata wancan, zai gamu da laifuffuka}
{A riɓanya masa azãba a Rãnar al-ƙiyãma. Kuma ya tabbata a cikinta yanã wulakantacce}
{Sai wanda ya tũba, kuma ya yi ĩmãni, kuma ya aikata aiki na ƙwarai to, waɗancan Allah Yanã musanya miyãgun ayyukansu da mãsu kyau. Allah Ya kasance Mai gãfara Mai jin ƙai} [al-Furƙan: 68-70], Kuma Allah - Maɗaukakin Sarki - Ya ce:
﴿وَهُوَ الَّذِي يَقْبَلُ التَّوْبَةَ عَنْ عِبَادِهِ وَيَعْفُو عَنِ السَّيِّئَاتِ وَيَعْلَمُ مَا تَفْعَلُونَ25﴾
{Kuma Shi ne ke karɓar tũba daga bãyinSa, kuma Yanã Yafe ƙananan laifuffuka, alhãli kuwa Yanã sanin abin da kuke aikatãwa} [al-Shura: 25].
Kuma ya inganta daga Manzon Allah -tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi- cewa ya ce: «Musulunci yana rusa abin da ya gabace shi, kuma tuba tana kankare abin da ya gabace ta».
Haƙiƙa na tace waɗannan kalmomin a taƙaice, saboda girman hatsarin shirka, da kuma kasancewar ta mafi girman zunubai, da kuma tsoron ruɗuwa da abinda ya fito daga wannan mai rubutun, kuma saboda wajibcin nasiha saboda Allah da kuma bayinSa. Ina roƙon Allah - girman Sa ya ɗaukaka -, Ya anfanar da wannan (bayani), kuma Ya kyautata halayan mu da halayan musulmai baki ɗaya, kuma Ya yi mana baiwa da fahimtar Addini da tabbata a kan sa, Ya kuma tsare mu da musulmai daga sharrukan kawunan mu da munanan ayyukan mu, Shi Majiɓincin hakan ne, kuma mai iko ne akan hakan.
Allah Yayi tsira da aminci da albarka ga bawanSa kuma ManzonSa Annabin mu Muhammad da alayensa da aahabbansa.
***
بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَنِ الرَّحِيمِ
SAƘO NA UKU
A cikin hukuncin neman taimako da aljanu da shaiɗanu da yin bakance gare su
Daga AbdulAzeez Bn Abdullahi Bn Baaz zuwa ga duk wanda ya gani daga cikin musulmai, Allah Ya datar da ni da su dan yin riƙo da addininSa da kuma tabbatuwa a kansa amin.
Amincin Allah a gareku da rahamarSa da albarkatunSa.
Bayan haka, haƙiƙa wani cikin ‘yan uwa ya tambaye ni akan wani abu da wasu jahilai suke aikatawa, na roƙon wanin Allah - tsarki ya tabbata a gare Shi -, da neman taimakon sa a muhimman abubuwa; kamar roƙon aljanu da neman agajin su, da yi musu alwashi da yi musu yanka. Daga wannan kuma zancen sashen su: (Ya Sab'atah), wato bakwai daga cikin shugabannin aljanu ku riƙe shi, ku karya ƙashin sa, ku sha jinin sa, ku daddatsa shi, Ya Sab’atah, ku aikata kaza da kaza da shi. Ko faɗin sashen su: (Ku kama shi ya ku aljanun tsakar rana, Ya ku aljanun la’asar), wannan akan same shi da yawa a ɓangaran kudanci. Yana kuma cikin abinda yake haɗuwa da wannan lamarin, kiran matattu daga cikin Annabawa da salihai da wasunsu, da kiran Mala’iku da kuma neman agajin su, Wannan fa gabaɗayan sa da ma ire-iren sa yana faruwa ne daga cikin masu jingina kansu da Musulinci, saboda sun jahilce shi, don kuma koyi da waɗanda suka gabace su, kuma akan sami wani daga sashen su ya ɗauki abin da sauƙi, har ma ya yi hujja akan hakan da cewa: Ai wannan abu ne da ke gudana a harshe, bamu nufatarsa, kuma bama ƙudurce shi.
Kuma ya tambaye ni: Game da hukuncin auran wanda aka san yana aikata waɗannan abubuwa, da (cin) yankan su, da yi musu sallah (idan sun mutu), haka (yin sallah) a bayan su, da kuma gaskata 'yan tsibbu da 'yan duba, kamar wanda yake da'awar sanin cuta da dalilanta ta hanyar kawai kallon wani abu daga cikin abinda ya taɓa jikin mara lafiya; kamar rawani da wando da mayafi da makamantan su.
Amsa ita ce: Godiya ta tabbata ga Allah Shi kaɗai, tsira da aminci su tabbata ga wanda babu wani Annabi a bayansa, da alayensa da sahabbansa da waɗanda suka shiriya da shiriyarsu har zuwa ranar sakamako.
Bayan haka: Lallai Allah - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka - Ya halicci mutane da aljanu don su bauta maSa, ba tare da bautawa waninSa ba, kuma su keɓance Shi da addu'a da neman taimako, da yanka da bakance da sauran ibadu, kuma Ya aiko Manzanni da wannan, kuma Ya umarce su da shi, Ya saukar da littattafan sama wanda mafi girma daga cikinsu shine Alƙur'ani mai girma da bayanin hakan da kuma kira zuwa gare shi, da gargaɗin mutane daga shirka da Allah da bautar waninSa. Wannan kuma shi ne asalin dukkan asalai, kuma tushen hanyar gaskiya da addini, kuma shi ne ma’anar shaidawa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, kuma haƙiƙanin: Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah. Ita kalmar shahada tana kore allantaka da ibadah ga wanin Allah, tana kuma tabbatar da ita - ai ibadah - ga Allah Shi kaɗai, banda waninSa daga sauran halittu, Dalilai akan wannan daga cikin littafin Allah da Sunnar ManzonSa - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - suna da matuƙar yawa, daga ciki: Faɗin Allah - girman Sa ya ɗaukaka -:
﴿وَمَا خَلَقْتُ الْجِنَّ وَالْإِنْسَ إِلَّا لِيَعْبُدُونِ56﴾
{Kuma Ban halitta aljannu da mutãne ba sai dõmin su bauta Mini} [al-Zariyat: 56], Da faɗinSa - tsarki ya tabbatar maSa -:
﴿وَقَضَى رَبُّكَ أَلَّا تَعْبُدُوا إِلَّا إِيَّاهُ...﴾
{Kuma Ubangijinka Ya hukunta kada ku bauta wa kõwa fãce Shi} [al-Isra'a: 23], Da faɗinSa - Maɗaukakin Sarki -:
﴿وَمَا أُمِرُوا إِلَّا لِيَعْبُدُوا اللَّهَ مُخْلِصِينَ لَهُ الدِّينَ حُنَفَاءَ...﴾
{Kuma ba a umarce su da kome ba fãce bauta wa Allah suna mãsu tsarkake addinin gare Shi, mãsu karkata zuwa ga addinin gaskiya} [al-Bayyinah: 5]. Da faɗinSa - Maɗaukakin Sarki -:
﴿وَقَالَ رَبُّكُمُ ادْعُونِي أَسْتَجِبْ لَكُمْ إِنَّ الَّذِينَ يَسْتَكْبِرُونَ عَنْ عِبَادَتِي سَيَدْخُلُونَ جَهَنَّمَ دَاخِرِينَ60﴾
{Kuma Ubangijinku ya ce: "Ku kira Ni in karɓa muku. Lalle waɗannan da ke kangara daga barin bauta Mini, za su shiga Jahannama sunã ƙasƙantattu} [Gafir: 60], Kuma Allah - Maɗaukakin Sarki - Ya ce:
﴿وَإِذَا سَأَلَكَ عِبَادِي عَنِّي فَإِنِّي قَرِيبٌ أُجِيبُ دَعْوَةَ الدَّاعِ إِذَا دَعَانِ...﴾
{Kuma idan bãyiNa suka tambaye ka daga gare Ni, to, lalle Ni Makusanci ne. Ina karɓa kiran mai kira idan ya kirā Ni} [al-Baƙara: 186].
Sai - tsarki ya tabbata a gare Shi - Ya bayyana a cikin waɗannan ayoyin cewa, Allah Ya halicci mutum da aljan ne domin su bauta masa, kuma Ya hukunta wato: Ya yi umarni da wasiyya ga bayinSa a ayoyin Alƙur'ani ingantattu, haka kuma akan harshen Manzo - tsira da aminci su tabbata a gare shi - cewa kada a bautawa kowa sai Ubangijin su.
Kuma (Allah) - Mai girma da ɗaukaka - Ya bayyana cewa addu'a ibada ce mai girma, wanda ya kangare daga gare ta zai shiga wuta, kuma ya umarci bayinsa su roƙe shi Shi kaɗai, kuma ya ba da labari cewa Yana kusa Yana amsa addu'arsu, don haka ya zama wajibi a kan dukkan bayi su keɓe Ubangijinsu da addu'a; domin ita nau'in ibada ce da aka halicce su don ta, kuma aka umarce su da ita, kuma (Allah) - Mai girma da ɗaukaka - Ya ce:
﴿قُلْ إِنَّ صَلَاتِي وَنُسُكِي وَمَحْيَايَ وَمَمَاتِي لِلَّهِ رَبِّ الْعَالَمِينَ162 لَا شَرِيكَ لَهُ وَبِذَلِكَ أُمِرْتُ وَأَنَا أَوَّلُ الْمُسْلِمِينَ163﴾
{Ka ce: "Lalle ne sallãta, da baikõna, da rãyuwãta, da mutuwãta, na Allah ne Ubangijin tãlikai"}
{Bãbu abõkin tãrayya a gare Shi. Kuma da wancan aka umurce ni, kuma ni ne farkon mãsu sallamãwa} [al-An'am: 162, 163].
Sai Allah Ya umarci AnnabinSa - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -, akan ya baiwa mutane labarin cewa sallar sa da baikon sa - shine yanka - da rayuwar sa da kuma mutuwar sa na Allah ne Ubangijin talikai ba Shi da abokin tarayya, gini akan hakan, duk wanda ya yi yanka ga wanin Allah to haƙiƙa ya yi wa Allah shirka, kamar da ace yayi sallah ga wanin Allah - Maɗaukakin Sarki -.; domin Allah - tsarki ya tabbata a gare Shi - Ya sanya sallah da yanka a tare, Ya kuma bada labarin cewa su din nan biyu na Allah ne Shi kadai, ba Shi da abokin tarayya. To duk wanda ya yi yanka ga wanin Allah daga aljanu, Mala’iku, matattu da sauransu, yana neman kusanci gare su, to kamar wanda ya yi sallah ne ga wanin Allah. Ya zo a cikin hadisi ingantacce cewa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: «Allah Ya tsinewa wanda yayi yanka dan wanin Allah». Imam Ahmad ya fitar (da hadisi) da isnadi mai kyau daga Ɗariƙ ɗan Shihab - Allah Ya yarda da shi - daga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - cewa shi ya ce: «Wasu mutum biyu sun wuce ta wurin wasu mutane da suke da wani gunki da ba wanda zai wuce shi sai ya miƙa masa wani abu dan neman kusanci, sai suka ce wa ɗaya daga cikinsu: Miƙa. Sai ya ce: Bani da wani abu da zan bayar, sai suka ce: Miƙo ko da ƙuda ne, sai ya bada wani ƙuda, sai suka barshi ya tafi, sai ya shiga wuta. Kuma suka ce wa ɗayan: Miƙo. Sai ya ce: Bazan miƙawa kowa wani abuba sai Allah - Mai girma da ɗaukaka - sai suka sare kansa, sai ya shiga Aljanna».
To idan wanda ya kasance yana neman kusanci ga gunki da makamancin shi da ƙuda da makamancin sa, yana zama mushriki, yana cancantar shiga wuta, to ya kake ganin wanda yake kiran aljanu da Mala’iku da waliyyai, to ya wanda yake neman agajin su yana musu bakance yana neman kusanta gare su da yanke-yanke, yana fatan tsarin dukiyarsa ko warakar da mara lafiyarsa ko amincin dabbobinsa da gonarsa, kuma ya ga wanda yake aikata hakan dan tsoron sharrin aljanu ko abinda ya yi kama da hakan.?!
Babu shakka duk wanda ya aikata haka da abubuwan da suke kama da hakan, shi ya fi cancantar zama mushiriki da ya cancanci shiga wuta akan wannan mutumin da ya gabatar da ƙuda ga gunki dan neman kusanci.
Daga cikin abinda ya zo a cikin wannan - kuma - faɗinSa - Maɗaukakin Sarki -:
﴿إِنَّآ أَنزَلۡنَآ إِلَيۡكَ ٱلۡكِتَٰبَ بِٱلۡحَقِّ فَٱعۡبُدِ ٱللَّهَ مُخۡلِصٗا لَّهُ ٱلدِّينَ2 أَلَا لِلَّهِ ٱلدِّينُ ٱلۡخَالِصُۚ وَٱلَّذِينَ ٱتَّخَذُواْ مِن دُونِهِۦٓ أَوۡلِيَآءَ مَا نَعۡبُدُهُمۡ إِلَّا لِيُقَرِّبُونَآ إِلَى ٱللَّهِ زُلۡفَىٰٓ إِنَّ ٱللَّهَ يَحۡكُمُ بَيۡنَهُمۡ فِي مَا هُمۡ فِيهِ يَخۡتَلِفُونَۗ إِنَّ ٱللَّهَ لَا يَهۡدِي مَنۡ هُوَ كَٰذِبٞ كَفَّارٞ3﴾
{Mun saukar da littafi a gareka da gaskiya sai ka bautawa Allah kana mai tsarkake Addini a gare Shi}
{To, addini tsarkakakke na Allah ne, kuma waɗanda suka riƙi waɗansu majibinta, bã Shi ba, (sunã cẽwa) "Ba mu bauta musu ba fãce dõmin su kusantar da mu zuwa ga Allah, kusantar daraja." Lalle Allah nã yin hukunci a tsakãninsu ga abin da suka zama sunã sãɓãwa a cikinsa. Lalle Allah ba Ya shiryar da wanda yake mai ƙarya, mai kãfirci} [al-Zumar: 1-3], Kuma Allah - Maɗaukakin Sarki - Ya ce:
﴿وَيَعْبُدُونَ مِنْ دُونِ اللَّهِ مَا لَا يَضُرُّهُمْ وَلَا يَنْفَعُهُمْ وَيَقُولُونَ هَؤُلَاءِ شُفَعَاؤُنَا عِنْدَ اللَّهِ قُلْ أَتُنَبِّئُونَ اللَّهَ بِمَا لَا يَعْلَمُ فِي السَّمَاوَاتِ وَلَا فِي الْأَرْضِ سُبْحَانَهُ وَتَعَالَى عَمَّا يُشْرِكُونَ18﴾
{Kuma sunã bautã wa, baicin Allah, abin da bã ya cũtar dasu kuma bã ya amfãninsu, kuma sunã cẽwa: "Waɗannan ne macẽtanmu a wurin Allah."Ka ce: "Shin, kunã bai wa Allah lãbãri ne, ga abin da bai sani ba, a cikin sammai ko a cikin ƙasa? TsarkinSa ya tabbata kuma Yã ɗaukaka daga abin da duk suke yin shirki da Shi."} [Yunus: 18].
Sai Allah - tsarki ya tabbata a gare Shi - Ya bada labari a cikin waɗannan ayoyi biyu, cewa mushirikai sun ɗauki wasu ba Allah ba majiɓinta daga cikin halittu, suna bauta musu tare da Shi (Allah) akan tsoro da fata da yanka da bakance da addu’a da makamancin haka, suna raya cewa waɗannan majiɓintan suna kusantar da waɗanda suka bauta musu zuwa ga Allah, kuma suna cetonsu a wurinSa. Sai Allah - tsarki ya tabbata a gare Shi - Ya ƙaryata su, Ya fayyace ƙaryarsu, Ya kuma kirasu maƙaryata, kafirai kuma mushirikai, Ya kuma tsarkake kanSa daga barin tarayya da Shi, sai Allah - Mai girma da ɗaukaka - Ya ce:
﴿...سُبْحَانَهُ وَتَعَالَى عَمَّا يُشْرِكُونَ﴾
{TsarkinSa ya tabbata kuma Yã ɗaukaka daga abin da duk suke yin shirki da Shi} [al-Nahl: 1]. Sai aka sani da wannan cewa, duk wanda ya riƙi wani mala'ika, ko Annabi ko aljani ko itace ko dutse yana kiransa tare da Allah, kuma yake neman taimakonsa, yana neman kusanci gare shi, da bakance da kuma yanka, da fatan samun cetonsa a wurin Allah, da kusantar da shi gare Shi, ko fatan warkar da mara lafiya, ko kiyaye dukiya, ko kuɓutar da wanda baya nan, ko makamancin haka; to haƙiƙa ya faɗa cikin shirka mai girma saboda wannan, da bala'i mai tsanani, wanda Allah Ya ce game da shi:
﴿إِنَّ اللَّهَ لَا يَغْفِرُ أَنْ يُشْرَكَ بِهِ وَيَغْفِرُ مَا دُونَ ذَلِكَ لِمَنْ يَشَاءُ وَمَنْ يُشْرِكْ بِاللَّهِ فَقَدِ افْتَرَى إِثْمًا عَظِيمًا48﴾
{Lalle ne, Allah ba Ya gãfarta a yi shirki game da Shi, kuma Yana gãfarta abin da yake bãyan wannan ga wanda Yake so, kuma wanda ya yi shirki da Allah, to, lalle ne ya ƙirƙiri zunubi mai girma} [al-Nisa'a: 48], Kuma Allah - Maɗaukakin Sarki - Ya ce:
﴿إِنَّهُ مَنْ يُشْرِكْ بِاللَّهِ فَقَدْ حَرَّمَ اللَّهُ عَلَيْهِ الْجَنَّةَ وَمَأْوَاهُ النَّارُ وَمَا لِلظَّالِمِينَ مِنْ أَنْصَارٍ72﴾
{Lalle ne shĩ, wanda ya yi shirki da Allah, to, lalle ne, Allah Yã haramta masa Aljanna. Kuma bãbu wasu mataimaka ga azzãlumai} [al-Ma'ida: 72].
Kuma ceto yana samuwa ne kawai a ranar Alƙiyama ga ma'abota tauhidi da ikhlasi, ba ga masu shirka ba, kamar yadda Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce lokacin da aka ce masa: Ya Manzon Allah, waye mafi arziƙin mutane da samun cetonka? sai ya ce: «Wanda ya ce: (Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah) yana mai ikhlasi daga zuciyarsa». Kuma - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: «Kowane Annabi yana da addu'ar da aka amsa masa, sai kowanne Annabi ya gaggauta addu'arsa, amma ni na ɓoye addu'a ta ta zama ceto ga al'ummata ranar Alƙiyama, kuma - in sha Allah - zata samu duk wanda ya mutu daga al'ummata ba tare da yayi shirka da Allah ba».
Kuma mushrikai na farko sun kasance suna imani da cewa Allah ne Ubangijinsu kuma Mahaliccinsu kuma Mai azurtarsu, kaɗai sun jingina ne ga annabawa da waliyyai da mala'iku da itatuwa da duwatsu da makamantan haka, suna fatan cetonsu a wurin Allah, da kusantar da su zuwa gare Shi, kamar yadda ya rigaya a cikin ayoyi, Allah Baiyi musu uzuri da hakan ba, bari ma dai, Allah Ya yi musu inkari a cikin littafinSa mai girma, Ya kuma kirasu kafirai da mushirikai, Ya kuma ƙaryata su a riyawar da suka yi akan cewar waɗannan allolin za su cecesu kuma za su kusantar da su ga Allah kusantarwa ta daraja. Haka Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - bai yi musu uzuri ba, bari ma dai, Manzon - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -, ya yaƙe su ne akan wannan shirkar har sai sun tsarkake ibada domin Allah shi kaɗai, don aiki da faɗinSa - tsarki ya tabbata a gare shi -:
﴿وَقَاتِلُوهُمْ حَتَّى لَا تَكُونَ فِتْنَةٌ وَيَكُونَ الدِّينُ لِلَّهِ...﴾
{Kuma ku yãƙe su har ya zama wata fitina bã zã ta kasance ba, kuma addini ya zama na Allah} [al-Baƙara: 193]. Kuma Manzo- tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: «An umurce ni da in yãƙi mutane har sai sun shaida cewa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah kuma cewa (Annabi) Muhammadu Manzon Allah ne, kuma su tsaida sallah, kuma su bayar da zakkah, to idan suka aikata haka sun tsare jinanansu da dukiyoyinsu daga gareni, sai dai bisa haƙƙin musulunci, kuma hisabinsu yana ga Allah». Ma'anar faɗin Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -: «Har sai sun shaida cewa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah» Wato: Har sai sun keɓe Allah da bauta, ba tare da waninSa ba.
Kuma haƙiƙa mushirikan sun kasance suna tsoron aljanu suna kuma neman tsari da su, sai Allah - Maɗaukakin Sarki - Ya saukar da faɗinSa akan hakan:
﴿وَأَنَّهُ كَانَ رِجَالٌ مِنَ الْإِنْسِ يَعُوذُونَ بِرِجَالٍ مِنَ الْجِنِّ فَزَادُوهُمْ رَهَقًا6﴾
{"Kuma lalle ne shi wasu maza daga cikin mutãne, sun kasance sunã nẽman tsari da wasu maza daga cikin aljannu, sabõda haka suka ƙara musu girman kai"} [al-Jin: 6]. Malaman tafsiri sun faɗi ma'anar faɗinSa: Akan wannan ayar mai girma:
﴿...فَزَادُوهُمْ رَهَقًا﴾
{"Sabõda haka suka ƙara musu girman kai"} Wato: firgici da tsoro; domin aljanu suna jin izza a kansu da girman kai, idan suka ga mutane suna neman tsari da su, a lokacin sai su ƙara musu tsoro da firgici, har sai sun ƙara yawan bautarsu, da fakewa gare su.
Kuma haƙiƙa Allah Ya mayar wa musulmai hakan ta hanyar neman tsari da Shi - tsarki ya tabbatar maSa -, da kuma cikakkun kalmominSa, kuma Ya saukar da wannan a cikin zancenSa - Maɗaukaki Sarki - inda Ya ce:
﴿وَإِمَّا يَنْزَغَنَّكَ مِنَ الشَّيْطَانِ نَزْغٌ فَاسْتَعِذْ بِاللَّهِ إِنَّهُ سَمِيعٌ عَلِيمٌ200﴾
{Kuma imma wata fizga daga Shaiɗan ta fizge ka, sai ka nẽmi tsari ga Allah. Lalle ne shi, Mai jĩ ne, Masani} [al-A'araf: 200], Da faɗinSa - Maɗaukakin Sarki -:
﴿قُلْ أَعُوذُ بِرَبِّ الْفَلَقِ1﴾
{Ka ce "ina neman tsari ga Ubangijin safiya"}, Kuma ya inganta daga annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - cewa ya ce: «Duk wanda ya sauka a wani masauki sai ya ce: (Ina neman tsari da kalmomin Allah cikakku daga sharrin abin da Ya halitta); wani babu bazai cutar da shi ba har ya bar masaukinsa wannan».
Daga cikin ayoyi da hadisan da suka gabata, mai neman tsira zai sani, kuma mai burin kiyaye Addininsa, da samun tsira daga shirka, zuzzurfinta da bayyanennenta, zai fahimci cewa dogaro da matattu da mala'iku da aljannu da wasunsu daga halittu, da kiran su da neman tsari da su da makamantan haka; yana daga cikin ayyukan mutanen Jahiliyya mushrikai, kuma yana daga cikin mafi munin shirka da Allah - tsarki ya tabbatar maSa -, don haka wajibi ne a bar shi, da kiyayewa daga wannan, da yiwa juna wasiyya da barin sa, da yin Allah wadai ga wanda ya aikata shi.
Amma wanda aka san shi a cikin mutane da irin waɗannan ayyukan na shirka, to ba ya halitta a aurar masa, haka ba ya halitta a ci yankansa haka yi masa sallah haka kuma sallah a bayansa, har sai ya bayyanar da tubansa ga Allah - Maɗaukakin sarki - akan hakan, ya tsarkake addu’ar sa da kuma tsarkake ibada ga Allah Shi kaɗai. Addu’a kuma ita ce ibada, a’a ita ce ma ɓargon (jigon) ta, kamar yadda Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: «Addu'a itace ibada». Kuma an ruwaito daga gare shi (Annabi) - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - a wani lafazin daban cewa ya ce: «Addu'a ita ce ɓargon (jigon) ibada». Amma aurar mushirikai: to haƙiƙa Allah - Maɗaukakin Sarki - Ya ce:
﴿وَلَا تَنْكِحُوا الْمُشْرِكَاتِ حَتَّى يُؤْمِنَّ وَلَأَمَةٌ مُؤْمِنَةٌ خَيْرٌ مِنْ مُشْرِكَةٍ وَلَوْ أَعْجَبَتْكُمْ وَلَا تُنْكِحُوا الْمُشْرِكِينَ حَتَّى يُؤْمِنُوا وَلَعَبْدٌ مُؤْمِنٌ خَيْرٌ مِنْ مُشْرِكٍ وَلَوْ أَعْجَبَكُمْ أُولَئِكَ يَدْعُونَ إِلَى النَّارِ وَاللَّهُ يَدْعُو إِلَى الْجَنَّةِ وَالْمَغْفِرَةِ بِإِذْنِهِ وَيُبَيِّنُ آيَاتِهِ لِلنَّاسِ لَعَلَّهُمْ يَتَذَكَّرُونَ221﴾
{Kuma kada ku auri mãtã mushirikai sai sun yi ĩmãni: Kuma lalle ne baiwa mũmina ita ce mafi alhẽri daga ɗiya kãfira, kuma kõ da tã bã ku sha'awa. Kuma kada ku aurar wa maza mushirikai sai sun yi ĩmãni, kuma lalle ne bãwa mũmini shi ne mafi alhẽri daga da mushiriki, kuma kõ da yã bã ku sha'awa, waɗannan suna kira ne zuwa ga wuta kuma Allah Yana kira zuwa ga Aljanna da gãfara da izninsa. Kuma Yana bayyana ãyõyinsa ga mutãne; tsammãninsu suna tunãwa} [al-Baƙara: 221], Sai Allah - tsarki ya tabbatar maSa -, Ya hana musulmai daga auren mãtã mushirikai, daga masu bautar gumãka da aljannu da mala'iku da sauran su, sai sunyi ĩmãni da tsarkake ibãda ga Allah Shi kaɗai, da gasgata Manzo, - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - a cikin abin da yazo da shi, da bin hanyar sa, kuma ya hana aurar mãza mushirikai ga mãtã Musulmai, sai sun yi ĩmãni da tsarkake ibãda ga Allah Shi kaɗai, da gasgata Manzo - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -, da kuma binsa.
Allah - tsarki ya tabbatar maSa - Ya bada labari cewa baiwa mumina tafi alheri daga 'yantacciyar mushrika, ko da ta burge wanda yake kalle ta, yake ji maganarta, saboda kyawunta da kyawun maganarta, kuma bawa mumini ya fi alheri daga 'yantaccen mushriki, ko da ya burge mai sauraro da mai kallon sa, saboda kyawunsa da fasaharsa da jarumtarsa da sauran su, sannan Ya bayyana dalilan wannan fifiko da fadinSa - tsarki ya tabbatar maSa -:
﴿...أُولَئِكَ يَدْعُونَ إِلَى النَّارِ...﴾
{Waɗannan suna kira ne zuwa ga wuta} [al-Baƙara: 221]. Yana nufin da wannan: Mushirikai maza da mushirikai mata; domin su na daga masu kira zuwa wuta da maganganunsu da ayyukansu da halayensu da ɗabi'unsu, amma muminai maza da muminai mata su na daga masu kira zuwa aljanna da ɗabi'unsu da ayyukansu da halayensu, to yaya waɗannan da waɗannan za su daidaita!
Amma yin sallah ga mushirikai (bayan mutuwarsu): to haƙiƙa Allah - Mai girma da ɗaukaka - Ya ce:
﴿وَلَا تُصَلِّ عَلَى أَحَدٍ مِنْهُمْ مَاتَ أَبَدًا وَلَا تَقُمْ عَلَى قَبْرِهِ إِنَّهُمْ كَفَرُوا بِاللَّهِ وَرَسُولِهِ وَمَاتُوا وَهُمْ فَاسِقُونَ84﴾
{Kuma kada ka yi salla a kan kõwa daga cikinsu wanda ya mutu, har abada, kuma kada ka tsaya a kan kabarinsa. Lalle ne sũ, sun kãfirta da Allah da ManzonSa, kuma sun mutu alhãli kuwa sunã fãsiƙai} [al-Taubah: 84], Sai (Allah) - Mai girma da ɗaukaka - Ya bayyana cikin wannan aya mai girma cewa ba za ayi sallah ga munafuki da kafiri ba; saboda kafircinsu ga Allah da ManzonSa, haka kuma ba za ayi sallah a bayansu, kuma ba za a sanya su shugabanni ga musulmai ba; saboda kafircinsu da rashin amincinsu, da kuma babbar adawa da ke tsakaninsu da musulmai, kuma saboda ba su daga cikin masu sallah da ibada; domin aiki baya wanzuwa a tare da kafirci da shirka, muna roƙon Allah Ya ba mu lafiya daga hakan. Amma kuma cin yankan mushirikai: to haƙiƙa Allah - girman Sa ya ɗaukaka - ya ce, Yana mai bayyana haramcin mushe da yankan mushirikai:
﴿وَلَا تَأْكُلُوا مِمَّا لَمْ يُذْكَرِ اسْمُ اللَّهِ عَلَيْهِ وَإِنَّهُ لَفِسْقٌ وَإِنَّ الشَّيَاطِينَ لَيُوحُونَ إِلَى أَوْلِيَائِهِمْ لِيُجَادِلُوكُمْ وَإِنْ أَطَعْتُمُوهُمْ إِنَّكُمْ لَمُشْرِكُونَ121﴾
{Kada ku ci daga abin da ba a ambaci sũnan Allah ba a kansa.* Kuma lalle ne shĩ fãsiƙanci ne. Kuma lalle ne, shaiɗãnu, haƙĩƙa, suna yin ishãra zuwa ga masõyansu, dõmin su yi jãyayya da ku. Kuma idan kuka yi musu ɗã'a, lalle ne kũ, haƙĩƙa, mãsu shirki ne} [al-An'am: 121], Sai Allah - girman Sa ya ɗaukaka - Ya hana musulmai cin mushe da yankan mushiriki; domin najasa ce, to yankansa yana da hukuncin mushe ne, ko da ya ambaci sunan Allah a yankan, domin ambaton Allah da ya yi a yankan ɓatacce ne ba shi da wani tasiri, domin hakan ibada ce, shirka kuma tana ɓata ibada ta lalata ta, har sai mushiriki ya tuba ya koma ga Allah - tsarki ya tabbata a gare shi -. Kaɗai - Maɗaukakin Sarki - Ya halatta abincin ma'abota littafi a cikin faɗinSa - tsarki ya tabbatar maSa -:
﴿...وَطَعَامُ الَّذِينَ أُوتُوا الْكِتَابَ حِلٌّ لَكُمْ وَطَعَامُكُمْ حِلٌّ لَهُمْ...﴾
{Kuma abincin waɗanda aka bai wa Littãfi halal ne a gare ku, kuma abincinku halal ne a gare su} [al-Ma'ida: 5], Saboda suna danganta kansu da Addini na sama, suna raya cewa su mabiyan Musa da Isa ne, duk da cewa ƙarya suke, kuma haƙiƙa Allah Ya shafe Addininsu Ya kuma soke shi da aiko Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ga mutane baki ɗaya, amma Allah - Mai girma da ɗaukaka - Ya halatta mana abincin Ahlul kitabi da (auren) matansu; saboda hikima mai girma da sirrika masu daraja, lallai malamai sun bayyana su, saɓanin mushrikai daga masu bautar gumaka da matattu, daga Annabawa da waliyyai da sauransu; domin Addininsu ba shi da asali, kuma babu shubha a cikin sa, bar dai, shi ɓatacce ne tun daga tushen sa, sai yankan mutanensa ya zama mushe, kuma cin sa ba ya halatta.
Amma faɗin mutum ga wanda yake yi wa magana: (Aljan ya same ka), (Aljan ya ɗauke ka), (Shaiɗan ya tashi da kai), da makamancin haka, wannan yana daga cikin zagi da tsinuwa, kuma hakan bai halatta tsakanin musulmi ba, kamar sauran nau'ikan zagi da tsinuwa, kuma wannan ba daga cikin shirka bane, sai dai idan mai faɗin hakan yana ƙudurcewa cewa aljanu suna tasarrafi a cikin mutane ba tare da izinin Allah da nufinSa ba. To duk wanda ya ƙudurce hakan a sha'anin aljannu ko waninsu daga cikin halittu, to kafiri ne da wannan ƙudurcewar, domin Allah - tsarki ya tabbatar maSa - Shine Mai mulki ga dukkan komai, kuma Mai iko akan dukkan komai, Shine Mai amfannarwa da cutarwa, kuma babu wani abu da za'a samar sai da izininSa da sonSa da ƙaddararSa mai gabatuwa, kamar yadda - Maɗaukakin sarki - Ya ce, yana mai umartar AnnabinSa tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi da ya sanar da mutane wannan babban asali:
﴿قُلْ لَا أَمْلِكُ لِنَفْسِي نَفْعًا وَلَا ضَرًّا إِلَّا مَا شَاءَ اللَّهُ وَلَوْ كُنْتُ أَعْلَمُ الْغَيْبَ لَاسْتَكْثَرْتُ مِنَ الْخَيْرِ وَمَا مَسَّنِيَ السُّوءُ إِنْ أَنَا إِلَّا نَذِيرٌ وَبَشِيرٌ لِقَوْمٍ يُؤْمِنُونَ188﴾
{Ka ce: "Bã ni mallaka wa raina wani amfãni, kuma haka ban tunkuɗe wata cũta, fãce abin da Allah Ya so. Kuma dã na kasance inã sanin gaibi, dã lalle ne, nã yawaita daga alhẽri kuma cũta bã zã ta shãfe ni ba, nĩ ban zama ba fĩce mai gargaɗi, kumamai bãyar da bishãra ga mutãne waɗanda suke yin ĩmãni} [al-A'araf: 188], Idan shugaban halitta kuma mafi alherinsu - tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi - ba ya mallakawa kansa wani amfani ko cuta, sai abinda Allah Ya ga dama, to ta yaya ga waninSa daga cikin halitta?! Kuma ayoyi masu yawa suna cikin wannan ma'ana.
Kuma tambayar ƴan duba da masu tsibbu da masana taurari da makamantansu, waɗanda suke da'awar bayar da labari akan abubuwan da suke ɓoye, to wannan abin ƙi ne da ba ya halatta, kuma gaskata su ya fi muni kuma ya fi zama abin ƙyama, har ma yana daga cikin rassan kafirci; saboda faɗin Annabi
- tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -: «Wanda ya je wurin ɗan duba ya tambaye shi wani abu; ba za a karɓi Sallarsa ta kwana arba’in ba». Muslim ne ya rawaito shi a cikin Sahih ɗin sa, Ya zo a cikin Sahihin sa - kuma - daga Mu'awiya bin al-Hakam al-Sulami -Allah Ya yarda da shi: «Cewa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya hana zuwa wajen bokaye da tambayar su».
Masu (littattafan) Sunan sun ruwaito daga annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - cewa shi ya ce: «Duk wanda yaje wajen boka, sai ya gasgata shi cikin abinda yake cewa; to haƙiƙa ya kafirta da abinda aka saukarwa (Annabi) Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -». Hadisai da suka zo da wannan ma’anar suna da yawa. Abinda yake wajibi a kan musulmi: Su yi hattara daga tambayar bokaye da masu duba, da sauran masu tsibbu, waɗanda suka shagala da bada labari game da gaibu, da yaudarar musulmi, ko da sunan magani ko wani abu daban, saboda abin da ya gabata na hani daga - Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -, da kuma tsawatarwar sa daga gare shi, Yana kuma shiga cikin hakan: Abinda wasu cikin mutane suke cewa da sunan ɗibbu (magani), na wasu lamurra na gaibu. Idan ya shinshina rawanin mara lafiya ko kallabin mara lafiya ko makamantan haka, sai ya ce: Wannan mara lafiyan ko mara lafiyar ya aikata abu kaza ko ya yi abu kaza, na abubuwan gaibu wanda ba ya jikin rawanin mara lafiyar da makamantan haka domin nuni akan hakan, kawai manufa akan hakan ita ce rikitar da mutane har ya kai ga mutane suke cewa: Ai masanin magunguna ne, da nau’ukan cututtuka da sabubban su, wataƙil ya ba su wasu abubuwa daga magunguna, kuma wataƙil ya dace da wannan warakar da ƙaddarar Allah, sai su yi tsmammanin ta sanadiyyar waɗannan magungunan nasa ne. Wataƙila rashin lafiya yana zuwa ne ta dalilin wasu aljanu da shaiɗanu, waɗanda suke hidimtawa wannan mai iƙirarin likitancin, kuma suna sanar da shi wasu daga cikin abubuwan gaibu waɗanda suke tsinkaye akan su, sai ya dogara da hakan, kuma ya gamsar da aljanu da shaiɗanu da abin da ya dace da su na ibada, sai su ɗauke kansu daga wannan mara lafiya, su bar abin da suka cuɗanya shi da shi yi na cutarwar, wannan sanannen abu ne game da aljanu da shaiɗanu da masu amfani da su.
Abinda yake wajibi akan musulmai kuma shi ne: A kiyayi haka, kuma a hana juna hakan, a kuma dogara ga Allah - tsarki ya tabbata a gare Shi -, da kuma dogaro gare Shi a dukkanin lamurra, babu laifi idan mutum ya yi Ruƙya (tofi na shari’a) da halastattun magunguna, da magani wurin likitoci waɗanda suke bincike ga mara lafiya da kuma tabbatarwa akan rashin lafiyar ta sa, ta hanyar zahiri da hankali, haƙiƙa ya inganta daga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - cewa ya ce : «Allah bai saukar da wata cuta ba, face ya saukar da waraka gare ta, wanda ya sani ya sani, wanda bai sani ba bai sani ba». Kuma - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: «Ga kowacce cuta an sanya mata magani, idan maganin ya haɗu da cutar, sai ya warke da izinin Allah». Kuma - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: «Ya bãyin Allah, ku nemi magani amma kada ku nemi mãgani da haram». Hadisai da suka zo da wannan ma’anar suna da yawa.
To muna roƙon Allah - girmanSa ya ɗaukaka -, da Ya gyara halayan musulmai baki ɗaya, Ya kuma warkar da zukatansu da jikinsu daga kowanne mugun abu, Ya kuma tara su akan shiriya, Ya kuma tsaremu da su daga fitintinu masu ɓatarwa, haka kuma ya tsare daga yi wa shaiɗan biyayya da majiɓantansa, lalle Shi (Allah) Mai iko ne akan komai, kuma babu ƙarfi babu dabara sai da (nufin) Allah - Mai ɗaukaka Mai girma -.
Allah Yayi tsira da aminci da albarka ga bawanSa kuma ManzonSa Annabin mu Muhammad da alayensa da aahabbansa.
***
بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَنِ الرَّحِيمِ
SAƘO NA HUƊU:
Akan hukuncin yin ibadah da wasu wuridai na bidi’a da na shirka
Daga AbdulAzeez Bn Abdullahi Bn Baaz zuwa ga ɗan'uwa mai daraja (.........), Allah Ya datar da shi ga dukkan alheri, amin.
Amincin Allah ya tabbata a gareku da rahamarSa da albarkatunSa.
Bayan haka: Haƙiƙa littafina mai daraja ya iso gare ku, Allah Ya haɗa ku da shiriyarSa, da abinda ya ƙunsa na fa'ida cewa akwai mutane waɗanda suke riƙon waɗansu wuridan da Allah bai saukar da wani dalili ba a kansu ba, daga cikinsu akwai wanda bidi'a ne, kuma akwai wanda shirka ne, kuma suna danganta hakan zuwa ga Amirul Muminin: Aliyu ɗan Abu Ɗalib - Allah Ya yarda da shi - da waninsa. Kuma suna karanta waɗannan zikiran a majalisai na zikiri, ko a masallatai bayan sallar magariba, suna zaton cewa hakan kusanci ne ga Allah, kamar faɗin su: Don haƙƙin Allah, Ya ku bayin Allah, ku taimake mu da taimakon Allah, kuma ku kasance taimakon mu don Allah. Kuma kamar faɗin su: Ya ƙuɗubai, ya shuwagabanni, ku amsa, ya masu madadi a cikinmu, ku yi ceto zuwa ga Allah, wannan bawan ku ne a tsaye, kuma a ƙofar ku yana mai kifuwa, kuma yana mai jin tsoro daga gazawarsa, ka taimake mu ya Manzon Allah, ba inda zanje in ba wurinku ba, kuma daga gare ku ne ake samun buƙata, kuma ku ne mutanen Allah, don Hamza shugaban shahidai, ya mamakin madadain da ake samu daga gurinku, ka taimake mu ya Manzon Allah. Kuma kamar faɗin su: Ya Allah Kayi salati ga wanda Ka sanya shi sanadiyyar buɗewar asiranKa na Aljabarut, kuma haskaka fitilun rahamarKa, har ya zama wakili daga halarar Ubangiji, kuma halifan asiranKa na zati.
Da kuma kwaɗayinku akan bayanin mecece bidi’a, kuma mecece shirka, kuma shin sallah ta yi idan aka yi ta bayan limamin da yake yin wannan addu’ar, dukkan wannan ya kasance sananne ne?.
Amsa ita ce: Godiya ta tabbata ga Allah Shi kaɗai, tsira da aminci su tabbata ga wanda babu wani Annabi a bayansa, da alayensa da sahabbansa, da kuma duk wanda ya shiryu da shiriyarsa har zuwa ranar sakamako.
Bayan haka: Ka sani - Allah Ya datar da kai - lallai Allah - tsarki ya tabbata a gareShi - kaɗai, Ya halicci halitta kuma Ya aiko manzanni - tsira da aminci su tabbata a gare su - dan a bauta maSa Shi kaɗai, ba Shi da abokin tarayya, banda dukkan waninSa, kamar yadda Allah - Maɗaukaki - Ya ce:
﴿وَمَا خَلَقْتُ الْجِنَّ وَالْإِنْسَ إِلَّا لِيَعْبُدُونِ56﴾
{Kuma Ban halitta aljannu da mutãne ba sai dõmin su bauta Mini} [al-Zariyat: 56].
Ibadah, - kamar yadda bayani ya gabata - ita ce: Biyayya ga Allah tsarki ya tabbata a gare Shi - da kuma biyayya ga Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -, ta hanyar aikata abinda Allah da ManzonSa suka yi umarni da shi, da kuma barin abinda Allah da Manzon Sa suka hana, na daga imani da Allah da ManzonSa, da tsarkake ibadah domin Allah a aiki, tare da kai ƙoli a son Allah, da cikar ƙanƙan da kai ga Allah Shi kaɗai banda wani wanda ba Shi ba; kamar yadda Allah - Maɗaukakin Sarki - Ya ce:
﴿وَقَضَى رَبُّكَ أَلَّا تَعْبُدُوا إِلَّا إِيَّاهُ...﴾
{Kuma Ubangijinka Ya hukunta kada ku bauta wa kõwa fãce Shi} [al-Isra'a: 23] Wato: Ya yi umarni kuma Ya yi wasiyya da a bauta maSa Shi kaɗai, Kuma Allah - Maɗaukakin Sarki - Ya ce:
﴿الْحَمْدُ لِلَّهِ رَبِّ الْعَالَمِينَ2 الرَّحْمَنِ الرَّحِيمِ3 مَالِكِ يَوْمِ الدِّينِ4 إِيَّاكَ نَعْبُدُ وَإِيَّاكَ نَسْتَعِينُ5﴾
{Godiya ta tabbata ga Allah Ubangijin halittu,
Mai rahama, Mai jin ƙai,
Mai nuna Mulkin Rãnar Sakamako,
{Kai kaɗai muke bautawa, kuma Kai kaɗai muke neman taimakonKa} [al-Fatiha: 2-5]. Sai Allah - Mai tsarki da ɗaukaka - Ya yi bayani a waɗannan ayoyin: Cewar Shine wanda Ya cancanci da a bauta masa Shi kaɗai, kuma a nemi taimakonSa Shi kaɗai. Allah - girmanSa ya ɗaukaka - Ya ce:
﴿إِنَّآ أَنزَلۡنَآ إِلَيۡكَ ٱلۡكِتَٰبَ بِٱلۡحَقِّ فَٱعۡبُدِ ٱللَّهَ مُخۡلِصٗا لَّهُ ٱلدِّينَ2 أَلَا لِلَّهِ ٱلدِّينُ ٱلۡخَالِصُۚ...﴾
{Mun saukar da littafi a gareka da gaskiya ka bautawa Allah kana mai tsarkake Addini a gare Shi.To, addini tsarkakakke na Allah ne}
To, addini tsarkakakke na Allah ne... [al-Zumar: 2-3]. Kuma Allah - Maɗaukakin Sarki - Ya ce:
﴿فَادْعُوا اللَّهَ مُخْلِصِينَ لَهُ الدِّينَ وَلَوْ كَرِهَ الْكَافِرُونَ14﴾
{Sabõda haka ku kirãyi Allah, kunã mãsu tsarkake addini a gare Shi, kuma kõ dã kãfirai sun ƙi} [Ghafir: 14], Kuma Allah - Maɗaukakin Sarki - Ya ce:
﴿وَأَنَّ الْمَسَاجِدَ لِلَّهِ فَلَا تَدْعُوا مَعَ اللَّهِ أَحَدًا18﴾
{Kuma lalle ne wurãren sujada na Allah ne, saboda haka kada ku kira kõwa tãre da Allah (da su, a cikinsu)} [al-Jinn: 18], Ayoyi a cikin wannan ma'ana suna da yawa, kuma dukkansu suna nuna wajabcin kaɗaita Allah da ibada.
Sanannen abu ne cewa ita addu’a da dukkanin nau’ukan ta ibadah ce, ba ya halatta ga wani daga mutane ya roƙi kowa face UbangijinSa, kuma ba zai roƙi wani ko ya nemi agajin wani ba saidai Allah (shi kaɗai), domin yin aiki da waɗannan ayoyin masu daraja, da kuma abinda ya zo a ma’anonin su. Wannan yana bayan abubuwan al'ada, da dalilan zahiri, wanda halitta mai rai gamu-ga-shi ke da iko akansu, domin waɗannan basa daga ibada, bari dai yana halatta da nassi da ijma'i cewa mutum zai iya neman taimako daga mutum mai rai mai iko, a cikin abubuwan al'ada da yake da iko akansu; kamar ya nemi taimako daga gareshi ko ya nemi agaji daga gareshi wajen kawar da sharri daga ɗansa ko bawansa ko karensa da makamantan haka, Kamar mutum ya neman agajin mutumin da yake a raye ne, yake a wurin kuma yake da iko (na yin agajin), ko wanda ba ya nan amma ta hanya da ake gani kamar rubutu da makamantansa, domin gina gidan sa ko gyaran motar sa ko abinda ya yi kama da haka. Yana daga hakan kuma: Neman agajin mutum da mutanen sa a jihadi da yaƙi da makamantan haka. Yana daga wannan babin kuma, faɗin Allah - Maɗaukakin Sarki - a ƙissar Annabi Musa -tsaira da aminci su tabbata a agare shi -:
﴿...فَاسْتَغَاثَهُ الَّذِي مِنْ شِيعَتِهِ عَلَى الَّذِي مِنْ عَدُوِّهِ...﴾
{Sai wannan da yake daga ƙungiyarsa ya nẽmi ãgajinsa akan wanda yake daga maƙiyansa} [al-Kasas: 15].
Amma neman agaji wurin matattu da aljan da Mala’iku da bishiyoyi da duwatsu, to duka wannan yana cikin babbar shirka, kuma yana cikin irin ayyukan mushirikan farko tare da allolinsu; kamar Uzza da Lata da wasunsu. Haka kuma neman agaji da taimako daga waɗanda ake ƙudircewa cewa waliyyai ne cikin rayayyu, a abinda babu mai iko a kansa sai Allah, kamar warkar da mara lafiya, shiryar da zukata, shiga aljannah da kuma tseratarwa daga wuta da makamantan haka.
Ayoyin da suka gabata da kuma abinda ya zo akan ma’anonisu na ayoyi da hadisai: Dukkan su suna nuni ne akan wajabcin fuskantar da zukata zuwa ga Allah a dukkanin lamurra, da kuma tsarkake ibadah domin Allah Shi kaɗai, domin an halicci bayi ne domin wannan, kuma da shine aka umarce su, - kamar yadda bayani ya gabata a ayoyin -, haka kuma kamar yadda Allah - tsarki ya tabbata a gare Shi - Ya ce:
﴿وَاعْبُدُوا اللَّهَ وَلَا تُشْرِكُوا بِهِ شَيْئًا...﴾
{Kuma ku bauta wa Allah kuma kada ku haɗa wani da Shi} [al-Nisa'a: 36], Da faɗinSa - tsarki ya tabbatar maSa -:
﴿وَمَا أُمِرُوا إِلَّا لِيَعْبُدُوا اللَّهَ مُخْلِصِينَ لَهُ الدِّينَ...﴾
{Kuma ba a umarce su da kome ba fãce bauta wa Allah suna mãsu tsarkake addinin gare Shi} [al-Bayyinah: 5], Da faɗin Annabi -tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi- a cikin Hadisin Mu'az -Allah Ya yarda da shi-: «Haƙƙin Allah a bisa bayi, su bauta maSa kada kuma su haɗa wani da Shi». Bukhari Da Muslim sun haɗu akan ingancinsa, Da faɗin sa - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce a cikin hadisin Ibn Mas'ud - Allah Ya yarda dashi -: «Duk wanda ya mutu yana kiran wani kishiya ga Allah, to zai shiga wuta». Bukhari ne ya rawaito shi. A cikin sahihai biyu (Bukhari da Muslim) daga hadisin ɗan Abbas - Allah Ya yarda da su - cewa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - lokacin da ya tura Mu'az zuwa Yamen, ya ce masa: «Lalle kai zaka je gun wasu mutane ma'abota littafi, to farkon abinda zaka fara kiransu zuwa garesa shine ya kasance; Shaidawa babu wani abin bauta da gaskiya sai Allah». A wani lafazin kuma: «Ka kira su zuwa ga shaidawa cewa babu abin bautawa da gaskiya sai Allah kuma lalle ni Manzon Allah ne». A wata riwayar ta Bukhari: «Sai ya kasance farkon abinda zaka kira su shi ne su kaɗaita Allah». Kuma a Sahih Muslim daga Ɗariƙ ɗan Ashyam al’Ashja’i, - Allah Ya yarda da shi -, cewa Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: «Duk wanda ya ce: Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah, ya kuma kafircewa abin da ake bautawa ba Allah ba; dukiyarsa da jininsa sun haramta, kuma hisabinsa yana ga Allah». Hadisai da suka zo da wannan ma’anar suna da yawa.
Kuma wannan TAUHIDIN shi ne asalin Addinin Musulinci kuma shi ne tushen aƙidah, shi ne kuma kan lamari kuma mafi girman farillai, shi ne kuma hikimar halittar mutum da aljan, da hikimar aiko Manzanni baki ɗaya -tsira da aminci su tabbata a gare su -, kamar yadda ayoyi masu nuni akan hakan suka gabata. Daga cikinsu: Faɗinsa - tsarki ya tabbata a gare Shi -:
﴿وَمَا خَلَقْتُ الْجِنَّ وَالْإِنْسَ إِلَّا لِيَعْبُدُونِ56﴾
{Kuma Ban halitta aljannu da mutãne ba sai dõmin su bauta Mini} [al-Zariyat: 56], Daga cikin dalilan haka - kuma -: FaɗinSa - Maɗaukakin Sarki -:
﴿وَلَقَدْ بَعَثْنَا فِي كُلِّ أُمَّةٍ رَسُولًا أَنِ اعْبُدُوا اللَّهَ وَاجْتَنِبُوا الطَّاغُوتَ...﴾
{Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun aika a cikin kõwace al'umma da wani Manzo (ya ce): "Ku bauta wa Allah, kuma ku nĩsanci ɗãgũtu} [al-Nahl: 36], da faɗinSa Allah - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka -:
﴿وَمَا أَرْسَلْنَا مِنْ قَبْلِكَ مِنْ رَسُولٍ إِلَّا نُوحِي إِلَيْهِ أَنَّهُ لَا إِلَهَ إِلَّا أَنَا فَاعْبُدُونِ25﴾
{Kuma ba Mu aiki wani Manzo ba a gabãninka fãce Munã yin wahayi zuwa gare shi, cẽwa "Lalle ne Shi, bãbu abin bautãwa fãce Nĩ, sai ku bauta Mini} [al-Anbiya: 25]. Kuma Allah - girmanSa ya ɗaukaka - Ya ce dangane da (Annabi) Nuhu da Hudu da Salihu da Shu’aibu - tsira da aminci su tabbata a gare su, cewa sun ce wa mutanensu:
﴿...اعْبُدُوا اللَّهَ مَا لَكُمْ مِنْ إِلَهٍ غَيْرُهُ...﴾
{Ku bauta wa Allah! Bã ku da wani abin bautãwa waninSa} [al-A'araf: 59], Wannan kuma ita ce da’awar Annabawa baki ɗaya, kamar yadda ayoyi biyun da suka gabata suka yi nuni akan hakan. Haƙiƙa maƙiya Manzanni sunyi iƙirari akan cewa Manzanni sun umarce su da su kaɗaita Allah da bauta, da yin watsi da duk wasu alloli da ake bautawa ba Allah ba, kamar yadda Allah - girmanSa ya ɗaukaka - Ya ce a cikin ƙissar Adawa, cewa sun faɗawa (Annabi) Hudu - tsira da aminci su tabbata a gare shi -:
﴿...أَجِئْتَنَا لِنَعْبُدَ اللَّهَ وَحْدَهُ وَنَذَرَ مَا كَانَ يَعْبُدُ آبَاؤُنَا...﴾
{Shin, kã zo mana ne dõmin mu bauta wa Allah Shi kaɗai, kuma mu bar abin da ubanninmu suka kasance sunã bauta wa} [al-A'araf: 70], Kuma (Allah) - tsarki ya taabata a gare Shi - Ya ce dangane da Ƙuraishawa a lokacin da Annabimmu Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya kira su akan su kaɗaita Allah da bauta, su kuma bar abinda suke bautawa ba Allah ba daga Mala’iku da waliyyai da gumaka da bishiyoyi da wanin haka:
﴿أَجَعَلَ الْآلِهَةَ إِلَهًا وَاحِدًا إِنَّ هَذَا لَشَيْءٌ عُجَابٌ5﴾
{Shin, yã sanya gumãka duka su zama abin bautawa guda? Lalle wannan, haƙĩƙa, abu ne mai ban mãmaki} [Saad: 5], Allah - Mai tsarki da ɗaukaka - Ya ce dangane da su:
﴿إِنَّهُمْ كَانُوا إِذَا قِيلَ لَهُمْ لَا إِلَهَ إِلَّا اللَّهُ يَسْتَكْبِرُونَ35 وَيَقُولُونَ أَئِنَّا لَتَارِكُوٓاْ ءَالِهَتِنَا لِشَاعِرٖ مَّجۡنُونِۭ36﴾
{Lalle sũ, sun kasance idan an ce musu: "Bãbu abin bautãwa, fãce Allah," sai su ɗõra girman kai}
Kuma sunã cẽwa, "Shin, mũ lalle mãsu barin gumãkanmu ne, sabõda maganar wani mawãƙi mahaukaci?) [al-Sāffāt: 35-36], Ayoyi masu nuni akan wannan ma’anar suna da yawa.
Daga cikin abinda muka ambata na ayoyi da hadisai, zai bayyana a gareka - Allah Ya datar da ni da kai ga fahimatar addini da kuma basira a haƙƙin Allah Ubangijin talikai - lalle waɗannan addu’o’in da nau’ikan neman agaji -, waɗanda na bayyana su a cikin tambayar ka, duka suna cikin nau’ikan babbar shirka; domin bauta ce ga wanin Allah, kuma neman wani abu ne da babu mai iko akansa in ba Shi ba, cikin matattu da waɗanda ba sa nan, wannan kuwa ta fi shirkar mutanen farko muni, domin mutanen farko suna shirka ne a lokacin wadata, Amma a lokacin tsanani, sai su tsarkake ibada ga Allah; domin su basa sanin cewa Shi - tsarki ya tabbatar maSa - shine mai ikon tsamosu daga tsanani ba wanin sa ba, kamar yadda Maɗaukakin Sarki Ya faɗa a cikin littafinSa mai bayyanawa game da waɗannan mushrikai:
﴿فَإِذَا رَكِبُواْ فِي ٱلۡفُلۡكِ دَعَوُاْ ٱللَّهَ مُخۡلِصِينَ لَهُ ٱلدِّينَ فَلَمَّا نَجَّىٰهُمۡ إِلَى ٱلۡبَرِّ إِذَا هُمۡ يُشۡرِكُونَ65﴾
{To, a lõkacin da suka shiga cikin jirgin ruwa, sun kirãyi Allah sunã mãsu tsarkake addini a gare shi, to, a lõkacin da Ya tsĩrar da su zuwa ga tudun ƙasã, sai gã su sunã shirki} [al-Ankabut: 65], Kuma - tsarki ya tabbatar maSa Ya ɗaukaka - Ya faɗa Yana yi musu magana a cikin wata ayar daban:
﴿وَإِذَا مَسَّكُمُ ٱلضُّرُّ فِي ٱلۡبَحۡرِ ضَلَّ مَن تَدۡعُونَ إِلَّآ إِيَّاهُۖ فَلَمَّا نَجَّىٰكُمۡ إِلَى ٱلۡبَرِّ أَعۡرَضۡتُمۡۚ وَكَانَ ٱلۡإِنسَٰنُ كَفُورًا67﴾
{Kuma idan cũta ta shãfe ku, a cikin tẽku, sai wanda kuke kira ya ɓace fãce Shi. To, a lõkacin da Ya tsira da ku zuwa, ga tudu sai kuka bijire. Kuma mutum ya kasance mai yawan butulci} [al-Isra'a: 67].
Idan mai magana ya ce, suwaye waɗannan mushirikan ‘yan baya: Lalle mu ba ma nufin waɗannan suna fa'idantarwa a karan kansu, kuma suna warkar da marasa lafiyarmu a karan kansu, ko suna amfanar damu a karan kansu, ko suna cutar damu a karan kansu ba, kawai abinda muke nufi shine cetansu a wurin Allah - Maɗaukakin Sarki - a cikin hakan?
Amsa: Ita ce, a ce masa: Wannan ai shi ne abin nufin kafiran farko kuma abin nemansu, ba wai suna nufin allolinsu suna halitta ne ko suna azurtawa ba, ko suna amfanarwa ko suna cutarwa ba a karan kansu, domin wannan abinda Allah Ya faɗa a cikin Alƙur'ani game da su yana ɓata shi. Lalle su sun nemi cetonsu ne da alfarmar su da kusantar da su ga Allah kusantarwa ta daraja, kamar yadda Allah - Maɗaukakin Sarki - Ya ce:
﴿وَيَعۡبُدُونَ مِن دُونِ ٱللَّهِ مَا لَا يَضُرُّهُمۡ وَلَا يَنفَعُهُمۡ وَيَقُولُونَ هَٰٓؤُلَآءِ شُفَعَٰٓؤُنَا عِندَ ٱللَّهِ...﴾
{Kuma sunã bautã wa, baicin Allah, abin da bã ya cũtar dasu kuma bã ya amfãninsu, kuma sunã cẽwa: "Waɗannan ne macẽtanmu a wurin Allah} [Yunus: 18], Sai Ya yi musu raddin wannan da faɗinSa:
﴿...قُلۡ أَتُنَبِّـُٔونَ ٱللَّهَ بِمَا لَا يَعۡلَمُ فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَلَا فِي ٱلۡأَرۡضِۚ سُبۡحَٰنَهُۥ وَتَعَٰلَىٰ عَمَّا يُشۡرِكُونَ﴾
{Ka ce: "Shin, kunã bai wa Allah lãbãri ne, ga abin da bai sani ba, a cikin sammai ko a cikin ƙasa? TsarkinSa ya tabbata kuma Yã ɗaukaka daga gabin da duk suke yin shirki da Shi"} [Yunus: 18], Sai (Allah) - tsarki ya tabbata a gare Shi - Ya yi bayanin cewa Shi Bai san wani mai ceto a wurinSa ba a cikin sammai da ƙasa ta wannan hanyar da mushirikai suke nufi. Kuma abinda Allah bai san shi ba to wannan abin ai babu shi; domin Shi (Allah) - tsarki ya tabbata a gare Shi - babu abinda yake ɓoyuwa a gare Shi. Kuma Allah - Maɗaukakin Sarki - Ya ce:
﴿تَنزِيلُ ٱلۡكِتَٰبِ مِنَ ٱللَّهِ ٱلۡعَزِيزِ ٱلۡحَكِيمِ 1 إِنَّآ أَنزَلۡنَآ إِلَيۡكَ ٱلۡكِتَٰبَ بِٱلۡحَقِّ فَٱعۡبُدِ ٱللَّهَ مُخۡلِصٗا لَّهُ ٱلدِّينَ2 أَلَا لِلَّهِ ٱلدِّينُ ٱلۡخَالِصُۚ وَٱلَّذِينَ ٱتَّخَذُواْ مِن دُونِهِۦٓ أَوۡلِيَآءَ مَا نَعۡبُدُهُمۡ إِلَّا لِيُقَرِّبُونَآ إِلَى ٱللَّهِ زُلۡفَىٰٓ إِنَّ ٱللَّهَ يَحۡكُمُ بَيۡنَهُمۡ فِي مَا هُمۡ فِيهِ يَخۡتَلِفُونَۗ إِنَّ ٱللَّهَ لَا يَهۡدِي مَنۡ هُوَ كَٰذِبٞ كَفَّارٞ3﴾
{Saukar da Littafin daga Allah ne, Mabuwãyi, Mai hikima,
Mun saukar da littafi a gareka da Gaskiya ka bautawa Allah kana mai tsarkake Addini a gare Shi,
To, addini tsarkakakke na Allah ne, kuma waɗanda suka riƙi waɗansu majibinta, bã Shi ba, (sunã cẽwa) "Ba mu bauta musu ba fãce dõmin su kusantar da mu zuwa ga Allah, kusantar daraja." Lalle Allah nã yin hukunci a tsakãninsu ga abin da suka zama sunã sãɓãwa a cikinsa. Lalle Allah ba Ya shiryar da wanda yake mai ƙarya, mai kãfirci} [al-Zumar: 1-3].
Kuma abinda ake nufi da addini anan: Ibada, kuma ita ce: ɗa'a ga Allah da ManzonSa tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - kamar yadda ya gabata. - Kuma yana shiga cikin ta: Addu’a da neman agaji da tsoro da ƙauna da yanka da alwashi, kamar kuma yadda sallah take shiga da azumi da wanin haka, cikin abinda Allah da ManzonSa suka yi umarni. Sai (Allah) - tsarki ya tabbata a gare shi - Ya yi bayanin lalle ita ibada, ta sa ce Shi kaɗai, kuma ya wajaba ga bayi su tsarkake ta gare Shi - girmanSa ya ɗaukaka -; domin umarninSa ga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare Shi - da tsarkake ibada gare Shi, umarni ne da ya shafi dukkan 'ya'yan wannan al’ummar.
Sannan Allah - Mai girma da ɗaukaka - Ya yi bayani bayan hakan dangane da kafirai, sai Ya ce:
﴿...وَٱلَّذِينَ ٱتَّخَذُواْ مِن دُونِهِۦٓ أَوۡلِيَآءَ مَا نَعۡبُدُهُمۡ إِلَّا لِيُقَرِّبُونَآ إِلَى ٱللَّهِ زُلۡفَىٰٓ...﴾
{Kuma waɗanda suka riƙi waɗansu majibinta, bã Shi ba, (sunã cẽwa) "Ba mu bauta musu ba fãce dõmin su kusantar da mu zuwa ga Allah, kusantar daraja} [al-Zumar: 3]. Sai Allah tsarki ya tabbata a gare shi - Ya yi musu raddi da faɗinSa - tsarki ya tabbata a gare Shi -:
﴿...إِنَّ ٱللَّهَ يَحۡكُمُ بَيۡنَهُمۡ فِي مَا هُمۡ فِيهِ يَخۡتَلِفُونَۗ إِنَّ ٱللَّهَ لَا يَهۡدِي مَنۡ هُوَ كَٰذِبٞ كَفَّارٞ﴾
{Lalle Allah nã yin hukunci a tsakãninsu ga abin da suka zama sunã sãɓãwa a cikinsa. Lalle Allah ba Ya shiryar da wanda yake mai ƙarya, mai kãfirci} [al-Zumar: 3], Sai Allah - tsarki ya tabbata a gare shi - Ya bayar da labari a cikin wannan ayar mai daraja: Cewa kafirai, ba su bautawa waliyyai ba koma bayan Allah sai domin su kusantar da su zuwa ga Allah kusantar daraja, wannan kuwa ita ce manufar na da, da na yanzu. Haƙiƙa Allah - Maɗaukakin Sarki - Ya ɓata hakan da faɗinSa:
﴿...إِنَّ ٱللَّهَ يَحۡكُمُ بَيۡنَهُمۡ فِي مَا هُمۡ فِيهِ يَخۡتَلِفُونَۗ إِنَّ ٱللَّهَ لَا يَهۡدِي مَنۡ هُوَ كَٰذِبٞ كَفَّارٞ﴾
{Lalle Allah nã yin hukunci a tsakãninsu ga abin da suka zama sunã sãɓãwa a cikinsa. Lalle Allah ba Ya shiryar da wanda yake mai ƙarya, mai kãfirci} [al-Zumar: 3], Sai Allah - tsarki ya tabbata a gare Shi - Ya bayyana ƙaryar su a rayawar su cewa, allolinsu zasu kusantar da su ga Allah kusantar daraja, kuma Ya kafirta su akan yadda suka karkatar musu da ibada, da wannan ne duk mai mafi ƙarancin fahimta zai san cewa kafiran farko kafircin su ya kasance ne ta ɗaukar Annabawa da waliyyai da itatuwa da duwatsu da wanin haka cikin halittu; dan nema masu ceto tsakaninsu da Allah, Da kuma ƙudircewarsu cewa suna biya musu buƙatunsu ba tare da izininSa da yardarSa - Maɗaukakin Sarki - ba, kamar yadda wazirai suke neman ceto a wurin shugabanni. Sai suka ƙiyasta Allah - Maɗaukakin sarki - da sarakuna da shuwagabanni. Suka kuma ce: Kamar yadda wanda yake da buƙata a wurin sarki da shugaba yake neman ceto izuwa gare shi ta hanyar keɓantattun mutanen sa da mataimakan sa, sai su ce to muma muna neman kusanci ga Allah ne da bautawa AnnabawanSa da WaliyyanSa, wannan kuwa yanan cikin mafi girman ɓarna; domin Shi (Allah) - tsarki ya tabbata a gare Shi - babu abinda ya yi kama da Shi, ba kuma a yin ƙiyasinSa da halittarSa, kuma babu wanda zai yi ceto a wurinSa sai da izinin Sa a ceton, kuma ba Ya yin izini sai ga masu Tauhidi, kuma shi tsarki ya tabbata a gare Shi - Mai iko ne akan komai, kuma Masani ne akan komai, Shine kuma mafi jinƙan masu jinƙai, ba Ya tsoron kowa babu mai razana shi; domin Shi (Allah) - tsarki ya tabbata a gare Shi -, Shi ne Mai iko akan bayinSa, kuma Shi ne Mai juya su kamar yadda Yake so. Saɓanin sarakuna da shuwagabanni, domin su ba su da iko akan komai, saboda haka suke buƙatar waɗanda zasu taimaka musu akan abinda suka kasa; cikin mataimakansu, da keɓantattun mutanensu da jami’an tsaron su, kamar yadda suke buƙatar isar musu da buƙatun wanda ba su san buƙatarsa ba, sai su buƙaci wanda zai tausaya musu, ya kwantar musu da hankali cikin mataimakansu da keɓantattun mutanensu, Amma Ubangiji - Mai girma da ɗaukaka -, Shi Mawadaci ne daga dukkan halittarSa, Shi ne Mafi jin kai a gare su fiye da iyayensu, Shi ne Mai adalci, Yana sanya ayoyi a wuraren da suka dace, bisa ga hikimarSa da iliminSa da ikonSa' Don haka, ba ya halatta a ƙiyasta Shi da halittarSa ta kowacce irin fuska. Saboda wannan ne (Allah) - tsarki ya tabbata a gare Shi - Ya fayyace a cikin littafinSa: Lalle mushirikai sun tabbatar da cewa shi ne Mahalicci Mai azurtawa Mai jujjuya lamurra, kuma Shi ne wanda Yake amsa addu’ar mabuƙaci, kuma Yake yaye damuwa, Ya ke rayawa kuma Yake kashewa, da wanin hakan daga ayyukanSa - tsarki ya tabbata a gare Shi -. Haƙiƙa husuma ta kasance tsakanin mushirikai da Manzanni akan tsarkake ibada domin Allah shi kaɗai, kamar yadda Allah -tsarki ya tabbata a gare Shi - Ya ce:
﴿وَلَئِن سَأَلۡتَهُم مَّنۡ خَلَقَهُمۡ لَيَقُولُنَّ ٱللَّهُ...﴾
{Kuma lalle idan ka tambaye su: "Wãne ne ya halitta su?" Lalle ne zã su ce Allah ne} [al-Zukhruf: 87], Kuma Allah - Maɗaukakin Sarki - Ya ce:
﴿قُلۡ مَن يَرۡزُقُكُم مِّنَ ٱلسَّمَآءِ وَٱلۡأَرۡضِ أَمَّن يَمۡلِكُ ٱلسَّمۡعَ وَٱلۡأَبۡصَٰرَ وَمَن يُخۡرِجُ ٱلۡحَيَّ مِنَ ٱلۡمَيِّتِ وَيُخۡرِجُ ٱلۡمَيِّتَ مِنَ ٱلۡحَيِّ وَمَن يُدَبِّرُ ٱلۡأَمۡرَۚ فَسَيَقُولُونَ ٱللَّهُۚ فَقُلۡ أَفَلَا تَتَّقُونَ31﴾
{Ka ce: "Wãne ne Yake azurtã ku daga sama da ƙasa? Shin kõ kuma Wãne ne Yake mallakar jĩ da ganĩ, kuma Wãne ne Yake fitar da mai rai daga mamaci, kuma Ya fitar da mamaci daga mai rai, Kuma Wãne ne Yake shirya al'amari?" To, zã su ce: "Allah ne." To, ka ce: "Shin fa, bã zã ku yi taƙawa ba?"} [Yunus: 31], Kuma ayoyi da suka zo da wannan ma’anar suna da yawa.
Haƙiƙa ya gabata: Ambton ayoyi masu nuni akan rikici tsakanin Annabawa da al’ummu abin sani kawai ya kasance ne akan tsarkake ibada ga Allah Shi kaɗai, kamar fadinSa Allah - tsarki ya tabbatar maSa -:
﴿وَلَقَدۡ بَعَثۡنَا فِي كُلِّ أُمَّةٖ رَّسُولًا أَنِ ٱعۡبُدُواْ ٱللَّهَ وَٱجۡتَنِبُواْ ٱلطَّٰغُوتَ...﴾
{Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun aika a cikin kõwace al'umma da wani Manzo (ya ce): "Ku bauta wa Allah, kuma ku nĩsanci ɗãgũtu} [al-Nahl: 36], Da kuma abinda ya zo a cikin ma’anarta na ayoyi. Kuma Allah - tsarki ya tabbata a gare Shi - Yayi bayanin sha'anin ceto a wurare masu yawa cikin littafinSa mai daraja, sai (Allah) - Maɗaukakin Sarki - Ya ce:
﴿َ...مَن ذَا ٱلَّذِي يَشۡفَعُ عِندَهُۥٓ إِلَّا بِإِذۡنِهِ...﴾
{Wane ne wanda yake yin cẽto a wurinSa, fãce da izninSa?} [al-Baƙara: 255], Kuma (Allah) - Mai girma da ɗaukaka - Ya ce-:
﴿وَكَم مِّن مَّلَكٖ فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ لَا تُغۡنِي شَفَٰعَتُهُمۡ شَيۡـًٔا إِلَّا مِنۢ بَعۡدِ أَن يَأۡذَنَ ٱللَّهُ لِمَن يَشَآءُ وَيَرۡضَىٰٓ26﴾
{Akwai malã'iku da yawa a cikin sammai cẽtonsu bã ya wadãtar da kõme fãce bãyan Allah Yã yi izni (da shi) ga wanda Yake so, kuma Yake yarda.} [al-Najm: 26].
Ya kuma ce a siffar Mala’iku:
﴿...وَلَا يَشۡفَعُونَ إِلَّا لِمَنِ ٱرۡتَضَىٰ وَهُم مِّنۡ خَشۡيَتِهِۦ مُشۡفِقُونَ﴾
{Kuma sũmasu sauna ne sabõda tsõron Sa} [al-Anbiya'a: 28].
Ya kuma bada labari - girmanSa ya ɗaukaka -, cewa Shi bai yardarwa bayinSa kafirci ba, abinda kawai Yake yarda da shi daga gare su shine godiya, godiyar kuma ita ce kaɗaita Shi da ibada da kuma yin aiki da biyayyar Sa, sai Allah - Maɗaukakin Sarki - Ya ce:
﴿إِن تَكۡفُرُواْ فَإِنَّ ٱللَّهَ غَنِيٌّ عَنكُمۡۖ وَلَا يَرۡضَىٰ لِعِبَادِهِ ٱلۡكُفۡرَۖ وَإِن تَشۡكُرُواْ يَرۡضَهُ لَكُمۡ...﴾
{Idan kun kãfirta to, lalle Allah Wadãtacce ne daga barinku, kuma bã Shi yarda da kãfirci ga bãyin Sa, kuma idan kun gõde, Zai yarda da ita (gõdiyar)} [al-Zumar: 7].
Kuma Bukhari ya ruwaito a cikin a sahihinsa daga Abu Hurairah - Allah Ya yarda da shi -, cewa ya ce: Ya Ma’aikin Allah! waye mafi rabauta da ceton ka a cikin mutane? (sai) ya ce: «Wanda ya ce: (Babu abin bautawa da gaskiya sai Allah) yana mai ikhlasi daga zuciyarsa». Ko ya ce: «Daga ransa».
Kuma ya zo a cikin sahih (na Bukhari) daga Anas - Allah Ya yarda da shi - daga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - cewa ya ce: «Kowane Annabi yana da addu'ar da aka amsa masa, sai kowanne Annabi ya gaggauta addu'ar sa, amma na ɓoye addu'a ta ta zama ceto ga al'umma ta ranar alƙiyama, kuma za ta samu - in sha Allah - duk wanda ya mutu daga al'umma ta ba tare da ya shirkanta komai da Allah ba». Hadisai da suka zo da wannan ma’anar suna da yawa.
Gabaɗayan abinda muka anbata na ayoyi da hadisai suna nuni ne akan ita ibada haƙƙin Allah ce Shi kaɗai, kuma ba ya halatta a karkatar da wani abu nata ga wanin Allah, ba ga Annabawa ba ko ga waninsu, kuma shi ceto mallakar Allah ne, kamar yadda Allah - tsarki ya tabbata a gare Shi - Ya faɗa:
﴿قُل لِّلَّهِ ٱلشَّفَٰعَةُ جَمِيعٗا...﴾
{Ka ce: "Cẽto gabã ɗaya ga Allah yake} [al-Zumar: 44] Babu wani da ya cancanci ceto sai bayan izinin Sa ga wanda zai yi ceton, da kuma yardarSa akan wanda za’a ceta, Shi kuma - tsarki ya tabbata a gare Shi - ba Ya yarda sai da Tauhidi, - kamar yadda ya gabata -. Gini akan hakan, lalle su mushirikai ba su da kaso a ceto, kuma haƙiƙa Allah Ya fayyace hakan a faɗinSa -Maɗaukakin Sarki -:
﴿فَمَا تَنفَعُهُمۡ شَفَٰعَةُ ٱلشَّٰفِعِينَ 48﴾
{Sabõda haka cẽton mãsu cẽto bã zai amfãne su ba} [al-Mudaththir: 48], Kuma Allah - Maɗaukakin Sarki - Ya ce:
﴿...مَا لِلظَّٰلِمِينَ مِنۡ حَمِيمٖ وَلَا شَفِيعٖ يُطَاعُ﴾
{Bãbu wani masõyi ga azzãlumai, kuma bãbu wani mai cẽto da zã a yi wa dã'a (ga cẽtonsu)} [Gafir: 18].
Kuma sananne ne cewa idan aka ambaci zalinci a sake, to shirka da Allah ake nufi, kamar yadda Allah - Maɗaukakin Sarki - Ya faɗa:
﴿...وَٱلۡكَٰفِرُونَ هُمُ ٱلظَّٰلِمُونَ﴾
{Kuma kãfirai sũ ne azzãlumai} [al-Baƙara: 254], Kuma Allah - Maɗaukakin Sarki - Ya ce:
﴿...إِنَّ ٱلشِّرۡكَ لَظُلۡمٌ عَظِيمٞ﴾
{Lalle shirki wani zãlunci ne mai girma} [Luƙman: 13].
Amma abinda ka ambata a cikin tambayar: Daga zancen wasu daga cikin Sufaye a cikin masallatai da waninsu: Ya Allah Ka yi salati ga wanda Ka sanya shi sababi na yayewar sirrikan Ka na Jabruti, kuma yayewa ga hasken Ka Rahamaniyya, sai ya kasance a madadin halartar Rabbaniyya, kuma halifan sirrikan Ka na zati…. izuwa ƙarshe.
Amsa: a ce: Lalle wannan maganar da ire irenta suna cikin zubin ɗorawa kai da shisshigi; wanda Annabinmu - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya hana; a abinda Muslim ya ruwaito a Sahih daga Abdullah ɗan Mas’ud - Allah Ya yarda da shi -, Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: «Masu tsattsauran ra'ayi sun halaka, ya faɗe ta sau uku.
Imam al-Khaɗɗabi - Allah Ya yi masa rahama - ya ce: Mai shisshigi: Mai kutsawa cikin abu, mai ɗorawa kai abu, mai ƙwaƙulo abun; akan tsarin ma'abota ilimin Kalam, masu shiga cikin abinda ba zai amfane su ba, masu kutsawa inda hakalinsu bai kaiba.
Abu al-Sa'adat Ibn al-Athir ya ce: Su ne masu zurfafawa masu guluwwi cikin magana, masu magana daga ƙololuwar maƙogwaron su, an samo shi ne daga kalmar 'Nuɗ'u' wanda shine rami mafi ɗaukaka a baki, sannan aka yi amfani da shi ga duk mai zurfafawa a magana da aiki.
Da kuma abinda waɗannan malaman biyu daga malaman Lugga suka ambata, zai bayyana a gareka da duk wanda yake da mafi ƙarancin hankali, lallai wannan tsari na salati da sallama ga Annabinmu kuma shugabanmu, Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - yana cikin jumallar ɗorawa kai da shisshigi wanda aka hana. Abinda aka shar’antawa musulmi a wannan batu shi ne, ya kardadi kaifiyya tabbatacciya daga Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -, a siffar yin salati da sallama a gare shi, wannan kuwa ya wadatar daga waninsa.
Daga cikin hakan: Abinda Bukhari da Muslim suka ruwaito a Sahihaini (Sahih al-Bukhari da Sahih Muslim) daga Ka’ab bn Ujrah - Allah Ya yarda da shi -, cewa sahabbai - Allah Ya yarda da su - sun ce: Ya Ma’aikin Allah, Allah Ya umarce mu mu yi maka salati; to yaya za mu yi maka salatin? Sai ya ce: «Ku ce:Ya Allah Kayi salati ga (Annabi) Muhammad da alayen (Annabi) Muhammad, kamar yanda Kayi salati ga (Annabi) Ibrahim da alayen (Annabi) Ibrahim, kuma Kayi albarka ga (Annabi) Muhammad da alayen (Annabi) Muhammad kamar yanda Kayi albarka ga (Annabi) Ibrahim da alayen (Annabi) Ibrahim, lallai Kai Abin yabo ne Mai girma».
Ya zo a cikin Sahihaini, daga Abu Humaid al-Sa’idi - Allah Ya yarda da shi -: Cewa sun ce: Ya Manzon Allah! Yaya za mu yi maka salati? (Sai) ya ce: «Ku ce: Ya Allah Kayi salati ga (Annabi) Muhammad da matayen sa da zuri'ar sa, kamar yanda Kayi salati ga alayen (Annabi) Ibrahim, kuma Kayi albarka ga (Annabi) Muhammad da matayen sa da zuri'ar sa, kamar yanda Kayi albarka ga alayen (Annabi) Ibrahim, lallai Kai Abin yabo ne Mai girma».
A cikin Sahih Muslim daga Abu Mas’ud al-Ansari, - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Bashir bn Sa’ad ya ce: Ya Ma’aikin Allah! Allah Ya umarce mu mu yi salati a gareka, to yaya za mu yi maka salatin? Sai ya yi shiru, sannan sai ya ce: «Ku ce: Ya Allah Ka yi salati ga (Annabi) Muhammad da alayen (Annabi) Muhammad; kamar yanda Ka yi salati ga alayen (Annabi) Ibrahim, kuma Ka yi albarka ga (Annabi) Muhammad, da alayen (Annabi) Muhammad; kamar yanda Ka yi albarka ga alayen (Annabi) Ibrahim. Lalle Kai abin yabo ne, Mai girma. Sai kuma sallama kamar yadda kuka sani».
To waɗannan lafuza da makamantansu da wasunsu, - daga abinda ya tabbata daga Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -, su ne waɗanda suka kamata mutum musulmi ya yi amfani da su a salatinsa da sallmarsa ga Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -, domin Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -, shi ne mafi sanin mutane da abinda ya cancanta a yi anfani da shi a haƙƙin sa, kamar kuma yanda yake mafi sanin mutane da abinda ya cancanta a yi amfani da shi na lafuza a haƙƙin Ubangijinsa da lafuza.
Amma lafuzan da aka ƙera da kuma sabbin lafuzai, da lafuzan da ke iya ɗaukar ma'ana mara inganci; kamar lafuzan da aka ambata a cikin tambaya, to bai kamata a yi amfani da su ba; saboda akwai sarƙaƙiya a cikin su, da kuma kasancewar ana iya fassara su da ma'anoni ɓatattu, tare da kasancewar su saɓanin lafuzan da Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya zaɓa, kuma ya shiryar da al'ummar sa izuwa gare su. Shi ne mafi sanin halitta kuma mafi nasihar su kuma mafi nisantar su daga sarƙaƙiya, - mafificin salati da aminci su tabbata a gare shi - daga Ubangijin sa.
Wannan kenan, ina fatan abinda muka ambata na dalilai a bayanin haƙiƙanin Tauhidi, da haƙiƙanin shirka, da kuma bambancin abinda mushirikan farko suke akai da mushirikai na baya a wannan babin, da bayanin kaifiyyar salati da aka shar’anta ga Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -, ya wadatar kuma ya gamsar da mai neman gaskiya. Amma wanda ba shi da kwaɗayin sanin gaskiya; wannan mai bin son ransa ne, Allah - Maɗaukakin Sarki - Ya ce:
﴿فَإِن لَّمۡ يَسۡتَجِيبُواْ لَكَ فَٱعۡلَمۡ أَنَّمَا يَتَّبِعُونَ أَهۡوَآءَهُمۡۚ وَمَنۡ أَضَلُّ مِمَّنِ ٱتَّبَعَ هَوَىٰهُ بِغَيۡرِ هُدٗى مِّنَ ٱللَّهِۚ إِنَّ ٱللَّهَ لَا يَهۡدِي ٱلۡقَوۡمَ ٱلظَّٰلِمِينَ50﴾
{To, idan ba su karɓa maka ba to sai ka sani sunã bin son zuciyarsu ne kawai, kuma wãne ne mafi ɓata daga wanda ya bi son zuciyarsa, bã tãre da wata shiriya daga Allah ba? Lalle ne, Allah bã ya shiryar da mutãne azzãlumai} [al-Ƙasas: 50].
Sai Allah - tsarki ya tabbta a gare Shi -, Ya yi bayani a cikin wannan ayar mai daraja: Cewa mutane dangane da abinda Allah Ya aiko Annabinsa Muhammad - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - na shiriya da addinin gaskiya, sun kasu kashi biyu:
Na farkonsu: Mai amsa wa Allah da ManzonSa ne.
Na biyu: Mai bin son zuciyarsa; sannan (Allah) - tsarki ya tabbata a gare Shi - Ya bada labarin cewa babu ɓatacce sama da wanda ya bi son zuciyar sa, ba tare da wata shiriya daga Allah ba.
Don haka muna roƙon Allah - girmanSa ya ɗaukaka - kiyayewa daga bin son zuciya, Ya kuma sanya mu da ku da sauran ‘yan uwanmu cikin waɗanda suka amsawa Allah da ManzonSa - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi -, kuma masu girmama shari’arSa, kuma masu tsawatarwa daga duk abinda ya saɓawa shari’arSa na bidi’a da son zuciya. Lalle Allah Mai kyauta ne kuma Mai karamci.
Allah Ya yi salati ga bawanSa kuma ManzonSa; Annabimmu Muhammad da alayensa da da sahabbansa da masu binsa da kyautatawa har izuwa ranar sakamako.
***